Acts
1Ya Tiyofalas, tarihin nan na farko wanda na rubuta, ya shafi dukan abubuwan da Yesu ya fara yi, da kuma waɗanda ya fara koyarwa, 2har ya zuwa ranar da aka ɗauke shi aka kai shi Sama, bayan da ya yi umarni ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa. 3Ya bayyana kansa gare su a raye bayan shan wuyarsa, tare da tabbatarwa masu yawa, masu ƙarfi kuma, yana bayyana a gare su a kai a kai har kwana arba'in, yana zancen al'amuran Mulkin Allah. 4Sa'ad da yake tare da su, ya umarce su kada su tashi daga Urushalima, amma su jira cikar alkawarin nan da Uba ya yi, “Wanda kuka ji daga bakina, 5domin Yahaya kam, da ruwa ya yi baftisma, amma kafin 'yan kwanaki da Ruhu Mai Tsarki za a yi muku baftisma.”
(Mar 16.19-20; Luka 24.50-53)
6Saboda haka da suka taru, suka tambaye shi suka ce, “Ya Ubangiji, yanzu ne za ka sāke kafa wa Isra'ila mulki?” 7Ya ce musu, “Sanin lokatai da zamanai, da Uba ya sa cikin ikonsa, ba naku ba ne. 8Amma za ku sami iko sa'ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauko muku, za ku kuma zama shaiduna a Urushalima, da duk ƙasar Yahudiya, da ta Samariya, har ya zuwa iyakar duniya.”
9Da ya faɗi haka, suna cikin dubawa, sai aka ɗauke shi Sama, wani gajimare ya tafi da shi, ba su ƙara ganinsa ba. 10Suna cikin zuba ido a sama, shi kuma yana tafiya, sai ga mutum biyu tsaye kusa da su, saye da fararen tufafi. 11Sai suka ce, “Ya ku mutanen Galili, don me kuke tsaye kuna duban sama? Yesun nan da aka ɗauke daga gare ku aka kai shi zuwa Sama, zai komo ne ta yadda kuka ga tafiyarsa zuwa Sama.”
12Sai suka koma Urushalima daga dutsen nan da ake kira Dutsen Zaitun, wanda yake kusa da Urushalima, wajen mil ɗaya. 13Da suka shiga birnin, suka hau soro inda suke zama, wato Bitrus, da Yahaya, da Yakubu, da Andarawas, da Filibus, da Toma, da Bartalamawas, da Matiyu, da Yakubu na Halfa, da Saminu Zaloti, da kuma Yahuza na Yakubu. 14Duk waɗannan da nufi ɗaya suka nace da addu'a, tare da mata, da Maryamu uwar Yesu, da kuma 'yan'uwansa.
15To, a kwanakin nan Bitrus ya miƙe tsaye cikin 'yan'uwa, (wajen mutum ɗari da ashirin ne a taron), ya ce, 16“Ya ku 'yan'uwana, lalle ne a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya faɗa a dā ta bakin Dawuda a game da Yahuza, wanda ya yi wa masu kama Yesu jagaba. 17Don an lasafta shi cikinmu dā, an kuma ba shi tasa hidima cikin aikin nan. 18(To, shi mutumin nan, da ladan mugun aikinsa ya sayi wani fili, sai ya fāɗi da kā, cikinsa ya fashe, kayan cikinsa duk suka zubo. 19Wannan abu fa ya zama sananne ga dukan mazaunan Urushalima, har ake kiran filin Akaldama harshensu, wato filin jini.) 20Domin a rubuce yake a Zabura cewa, “‘Gidansa yă zama yasasshe, Kada kowa ya zauna a ciki.” Da kuma, “‘Matsayinsa wani yă gada.” 21Don haka, lalle wani daga cikin mutanen nan da suke tare da mu, duk lokacin da Ubangiji Yesu yake cuɗanya da mu, 22tun daga baftismar da Yahaya ya yi, har ya zuwa ranar da aka ɗauke shi daga wurinmu aka kai shi zuwa Sama, wato ɗaya daga cikin mutanen nan ya zama shaidar tashinsa daga matattu, tare da mu.” 23Sai suka nuna mutum biyu, Yusufu mai suna Barsaba, wanda aka yi wa laƙabi da Yustus, da kuma Matiyas. 24Sai suka yi addu'a, suka ce, “Ya Ubangiji, masanin zuciyar kowa, a cikin waɗannan mutum biyu ka nuna wanda ka zaɓa, 25yă karɓi matsayi cikin aikin nan da manzancin nan da Yahuza ya bauɗe wa, don yă cike gurbinsa.” 26Sai suka yi musu kuri'a, Matiyas ya ci, aka kuma sa shi a cikin manzannin nan goma sha ɗaya.
1Da ranar Fentikos ta yi, duk suna tare a wuri ɗaya, 2farat ɗaya, sai aka ji wani amo daga sama, kamar na busowar gawurtacciyar iska, ya cika duk gidan da suke zaune. 3Sai waɗansu harsuna kamar na wuta suka bayyana a gare su, suna rarrabuwa, suna sassauka a kan ko wannensu. 4Sai duk, aka cika su da Ruhu Mai Tsarki, suka kuma fara magana da waɗansu harsuna dabam dabam, gwargwadon yadda Ruhun ya yi musu baiwar yin magana.
5To, a Urushalima a lokacin, akwai waɗansu Yahudawa masu bautar Allah daga ko'ina cikin ƙasashen duniya. 6Da jin dirin nan kuwa, taron ya haɗe, ya ruɗe, domin ko wannensu ya ji suna magana da harshen garinsu. 7Sai suka yi al'ajabi suka yi mamaki, suna cewa, “Ashe, duk masu maganar nan ba Galilawa ba ne? 8Ƙaƙa kuwa ko wannenmu yake ji da harshen garinsu ake magana? 9Ga mu kuwa, Fartiyawa, da Madayanawa, da Elamawa, da mutanen ƙasar Bagadaza, da ne Yahudiya, da na Kafadokiya, da na Fantas, da na Asiya, 10da na Firijiya, da na Bamfiliya, da na Masar, da kuma na kewayen Kurane ta ƙasar Libiya, har ma da baƙi daga Roma, wato Yahudawa, da kuma waɗanda suka shiga Yahudanci, 11da kuma Karitawa, da Larabawa, duk muna ji suna maganar manyan al'amuran Allah da harshen garuruwanmu.” 12Duk kuwa suka yi mamaki, suka ruɗe, suna ce wa juna, “Me ke nan kuma?” 13Amma waɗansu suka yi ba'a suka ce, “Ruwan inabi suka sha suka yi tatil!”
14Amma Bitrus ya miƙe tare da sha ɗayan nan, ya ɗaga murya ya yi musu jawabi, ya ce, “Ya ku 'yan'uwana Yahudawa da dukan mazaunan Urushalima, ku kula da wannan, ku kuma saurari maganata. 15Ai, mutanen nan ba bugaggu ba ne yadda kuke zato, tun da ya ke yanzu ƙarfe tare na safe ne kawai. 16Wannan, ai, shi ne abin da Annabi Yowel ya faɗa cewa, 17“‘Allah ya ce, A zamanin karshe zai zamanto zan zubo wa dukan 'yan adam Ruhuna. 'Ya'yanku mata da maza za su yi annabci, Wahayi zai zo wa samarinku, Dattawanku kuma za su yi mafarkai. 18Hakika, har ma a kwanakin nan zan zubo Ruhuna a kan bayina mata da maza, Za su kuma yi annabci. 19Zan nuna abubuwan al'ajabi a sararin sama, Da mu'ujizai a nan ƙasa, Wato jini, da wuta, da kuma, hauhawan hayaƙi. 20Za a mai da rana duhu, Wata kuma jini, Kafin Ranar Ubangiji ta zo, Babbar ranar nan mai girma. 21A sa'an nan ne zai zamanto kowa ya yi addu'a da sunan Ubangiji zai sami ceto.”
22“Ya ku 'yan'uwa, Isra'ilawa, ku ji wannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar muku cewa shi yardajjensa ne, ta mu'ujizai, da abubuwan al'ajabi, da alamu waɗanda ya yi ta wurinsa a cikinku, kamar yadda ku kanku kuka sani, 23shi Yesun nan fa, an ba da shi bisa ƙaddarar Allah da rigyasaninsa, ku kuwa kuka gicciye shi, kuka kashe shi, ta hannun masu zunubi. 24Amma Allah ya tashe shi bayan ya ɓalle masa ƙangin mutuwa, domin ba shi yiwuwa mutuwa ta riƙe shi. 25Dawuda kuma ya yi faɗi a game da shi ya ce, “‘Kullum hankalina yana kan Ubangiji, Yana damana, domin kada in jijjigu. 26Saboda haka, zuciyata ta yi fari, ina farin ciki matuƙa. Ko da yake kuma ni jiki ne, zan zauna ina sa zuciya, 27Domin ba za ka yar da raina a Hades ba, Ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka ya ruɓa ba. 28Kā sanar da ni hanyoyin rai. Za ka cika ni da farin ciki ta zamana a zatinka.” 29Ya 'yan'uwa, na iya yi muku magana da amincewa a game da kakanmu Dawuda, cewa ya mutu, an binne shi, kabarinsa kuma yana nan gare mu har ya zuwa yau. 30To, da ya ke shi annabi ne, ya kuma san Allah ya rantse masa, cewa zai ɗora wani daga cikin zuriyarsa kan kursiyinsa, 31sai ya hango, ya kuma yi faɗi a kan tashin Almasihu daga matattu, cewa ba za a yashe shi a Hades ba, jikinsa kuwa ba zai ruɓa ba. 32Yesun nan kam, Allah ya tashe shi daga matattu, mu kuwa duk shaidu ne ga haka. 33Da yake an ɗaukaka shi a dama ga Allah, ya kuma sami cikar alkawarin nan na baiwar Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, sai ya zubo da wannan da kuke gani, kuke kuma ji. 34Ai, ba Dawuda ne ya hau Sama ba, amma shi kansa ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, Zauna a damana, 35Sai na sa ka tāke maƙiyanka.”
36“Don haka sai duk jama'ar Isra'ila su sakankance, cewa shi Yesun na da kuka gicciye, Allah ya mai da shi Ubangiji, da kuma Almasihu.”
37To, da suka ji haka, maganar ta soke su a zuci, suka ce wa Bitrus da sauran manzannin, “'Yan'uwa, me za mu yi?” 38Sai Bitrus ya ce musu, “Sai ku tuba, a yi wa ko wannenku baftisma, a kan kun yarda da sunan Yesu Almasihu, domin a gafarta zunubanku, za ku kuwa sami baiwar Ruhu Mai Tsarki, 39domin alkawarin nan ku aka yi wa, ku da 'ya'yanku, da kuma dukan manisanta, wato duk waɗanda Ubangiji Allahnmu ya kira.” 40Sai ya yi ta tabbatar musu da maganganu masu yawa, yana ta yi musu gargaɗi, yana cewa, “Ku tserar da kanku daga wannan karkataccen zamani.” 41Waɗanda suka ya na'am da maganarsa kuwa aka yi musu baftisma. A ran nan kuma suka ƙaru da mutum wajen dubu uku. 42Sai suka himmantu ga koyarwar manzanni da tarayya da juna, da gutsuttsura gurasa, da kuma yin addu'a.
43Sai tsoro ya kama kowa, aka kuma yi abubuwan al'ajabi da mu'ujizai da yawa ta wurin manzannin. 44Dukan masu ba da gaskiya suna tare, suna mallakar kome nasu gaba ɗaya. 45Suka sayar da mallakarsu da kayansu, suka rarraba wa kowa kuɗin, gwargwadon bukatarsa. 46Kowace rana kuma sukan riƙa zuwa Haikali da nufi ɗaya, suna gutsuttsura gurasa a gidajensu, suna cin abinci da farin ciki ƙwarai, rai kwance, 47suna yabon Allah, suna da farin jini a wurin dukan mutane. Kowace rana kuma Ubangiji yana ƙara masu waɗanda ake ceta.
1To, Bitrus da Yahaya suna tafiya Haikali a lokacin addu'a, da ƙarfe uku na yamma, 2sai ga wani mutum da aka haifa gurgu, ana ɗauke da shi. Kowace rana kuwa akan ajiye shi a ƙofar Haikali, wadda ake kira Ƙawatacciyar Ƙofa, don ya roƙi sadaka ga masu shiga Haikali. 3Da ganin Bitrus da Yahaya suna shiga Haikalin, ya roƙe su sadaka. 4Bitrus kuwa ya zuba masu ido, tare da Yahaya, ya ce, “Dube mu.” 5Sai kuwa duk hankalinsa ya koma a kansu, da tsammanin samun wani abu a gunsu. 6Amma Bitrus ya ce, “Kuɗi kam, ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. Da sunan Yesu Almasihu Banazare, yi tafiya.” 7Sai Bitrus ya kama hannunsa na dama, ya tashe shi. Nan tāke ƙafafunsa da wuyan sawunsa suka yi ƙarfi. 8Wuf, sai ya zabura, ya miƙe tsaye, ya fara tafiya, ya shiga Haikalin tare da su, yana tafe, yana tsalle, yana kuma yabon Allah. 9Duk mutane suka gan shi yana tafe yana yabon Allah. 10Suka kuwa gane shi ne mai zama a bakin Ƙawatacciyar Ƙofa ta Haikali yana bara. Sai mamaki ya kama su, suna al'ajabi ƙwarai a kan abin da aka yi masa.
11Tun yana riƙe da Bitrus da Yahaya, duk jama'a suka sheƙa a guje zuwa wurinsu a cikin shirayin da ake kira Shirayin Sulemanu, suka ruɗe don mamaki. 12Da Bitrus ya ga haka, sai ya yi wa jama'a jawabi, ya ce, “Ya ku 'yan'uwa Isra'ilawa, don me kuke mamakin wannan? Don me kuma kuke ta dubanmu, sai ka ce da ikon kanmu ne, ko kuwa don ibadarmu muka sa shi tafiya? 13Allahn Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allahn kakanninmu, shi ya ɗaukaka Baransa Yesu, wanda kuka bashe shi, kuka kuma ƙi shi, a gaban Bilatus, sa'ad da ya ƙudura zai sake shi. 14Amma ku kuka ƙi Mai Tsarkin nan, mai adalci kuka roƙa a saukar muku da mai kisankai, 15kuka kuwa kashe Tushen Rai, amma Allah ya tashe shi daga matattu, mu kuwa shaidu na ga haka. 16To, sunansa ne, wato ta wurin bangaskiya ga sunansa, shi ne ya ba mutumin nan da kuke gani, kuka kuma sani, ƙarfi. Hakika, bangaskiyar da take ta wurin Yesu ita ta ba mutumin nan cikakkiyar lafiya, a gaban idonku duka.
17“To, yanzu 'yan'uwa, na sani da jahilci kuka yi haka, kamar yadda shugabanninku ma suka yi. 18Amma ta haka Allah ya cika faɗar da ya riga ya yi ta bakin annabawa duka, cewa Almasihunsa zai sha wuya. 19Saboda haka sai ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, Ubangiji kuma kansa ya riƙa wartsakar da ku, 20ya kuma aiko da Almasihun da aka ƙaddara muku tun dā, wato Yesu, 21wanda lalle ne ya zauna a Sama, har kafin lokacin nan na sabunta dukkan abubuwa da Allah ya faɗa tun zamanin dā ta bakin annabawansa tsarkaka. 22Musa ma ya ce, “‘Ubangiji Allah zai tasar muku da wani annabi daga cikin 'yan'uwanku, kamar yadda ya tashe ni. Lalle ne ku saurari duk abin da ya faɗa muku. 23Zai zamana kuma duk wanda ya ƙi sauraron annabin nan, za a hallaka shi daga cikin jama'a.” 24Hakika dukan annabawa da suka yi annabci, wato tun daga kan Sama'ila da waɗanda suka zo daga baya, duk sun yi faɗi a kan waɗannan kwanakin. 25Ku ne tsatson annabawa, ku ne kuma magadan alkawarin da Allah ya yi wa kakanninku, da ya ce wa Ibrahim, “‘Ta zuriyarka ne za a yi wa dukkan kabilan duniya albarka.” 26Da Allah ya taso da Baransa, gare ku ne ya fara aiko shi, don yă yi muku albarka ta juyo da ko wannenku ga barin muguntarsa.”
1Suna cikin yin magana da jama'a sai firistoci da shugaban dogaran Haikali da Sadukiyawa suka ji haushi ƙwarai, suka aukar musu, 2don suna koya wa jama'a, suna tabbatar da tashi daga matattu, suna misali da Yesu. 3Sai suka kama su, suka sa su a gidan waƙafi kafin gobe, don magariba ta riga ta yi. 4Amma da yawa daga cikin waɗanda suka ji wa'azin sun ba da gaskiya, har jimillarsu ta kai wajen mutum dubu biyar.
5Kashegari shugabanninsu da dattawansu da malamansu na Attaura suka taru a Urushalima, 6tare da Hanana, babban firist, da Kayafa, da Yahaya, da Iskandari, da kuma duk waɗanda suke dangin babban firist. 7Da suka tsai da su a tsakiya, suka tuhume su, suka ce, “Da wane iko ne, ko kuwa da wane suna ne, kuka yi haka?” 8Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya ce musu, “Ya ku shugabannin jama'a, da dattawa, 9in dai ana tuhumarmu ne yau a kan alherin da aka yi wa gajiyayyen mutumin nan, ta yadda aka warkar da shi, 10to, sai ku sani, ku duka, da kuma duk jama'ar Isra'ila, da sunan Yesu Almasihu Banazare, wanda ku kuka gicciye, wanda kuma Allah ya tashi shi daga matattu, albarkacinsa ne mutumin nan yake tsaye a gabanku lafiyayye. 11Wannan shi ne dutsen nan da ku magina kuka raina, shi ne kuwa ya zama mafificin dutsen gini. 12Ba kuma samun ceto ga wani, domin ba wani suna duk duniyar nan da aka bayar cikin mutane, wanda lalle ta wurinsa ne za mu sami ceto.”
13To, da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yahaya, suka kuma gane marasa ilimi ne, talakawa kuma, suka yi mamaki, suka kuwa shaida su, a kan dā suna tare da Yesu. 14Amma da suka ga mutumin nan da aka warkar ɗin yana tsaye tare da su, suka rasa hanyar yin mūsu. 15Bayan sun umarce su, su fita daga majalisa, suka yi shawara da juna, 16suka ce, “Yaya za mu yi da mutanen nan? Don hakika sanannen abu ne ga dukan mazauna Urushalima, cewa an yi wata tabbatacciyar mu'ujiza ta wurinsu, ba mu kuwa da halin yin mūsu. 17Amma don kada abin ya ƙara bazuwa a cikin mutane, sai mu yi musu kashedi, kada su kuskura su ƙara yi wa kowa magana, suna kama wannan suna.” 18Sai suka kirawo manzannin, suka kwaɓe su, kada su kuskura su yi wa kowa magana, ko su ƙara koyarwa suna kama sunan Yesu. 19Amma Bitrus da Yahaya suka mayar musu da jawabi suka ce, “To, in daidai ne a gun Allah mu fi jin taku da ta Allah, sai ku duba ku gani. 20Domin mu kam, ba yadda za a yi sai mun faɗi abin da muka ji, muka kuma gani.” 21Da kuma suka daɗa yi musu kashedi, suka sake su, don sun rasa yadda za su hore su saboda jama'a, domin dukan mutane suna ɗaukaka Allah saboda abin da ya auku. 22Mutumin nan da aka yi wa mu'ujizar nan ta warkarwa kuwa ya ba shekara arba'in baya.
23Da aka săke su, suka tafi wurin mutanensu, suka ba su labarin duk abin da manyan firistoci da shugabanni suka faɗa musu. 24Su kuwa da jin haka, sai suka ɗaga muryarsu ga Allah da nufi ɗaya, suka ce, “Ya Mamallaki, Mahaliccin sama, da ƙasa, da teku, da kuma dukkan abin da yake a cikinsu, 25wanda ta Ruhu Mai Tsarki, ta bakin kakanmu Dawuda baranka, ka ce, “‘Don me al'ummai suka husata? Kabilai kuma suka yi makidar al'amuran wofi>
26Sarakunan duniya sun kafa dāga, Mahukunta kuma sun haɗa kai, Suna gāba da Ubangiji, da kuma Almasihunsa.”
27Gama hakika Hirudus da Buntus Bilatus sun haɗa kai a birnin nan tare da al'ummai da jama'ar Isra'ila gāba da Yesu Baranka mai tsarki, wanda ka maishe shi Almasihu. 28Sun haɗa kai domin su yi dukan abin da ka ƙaddara zai auku, bisa ga ikonka da nufinka. 29Yanzu kuma ya Ubangiji, dubi wannan kashedinsu, ka yi wa bayinka baiwar yin maganarka da iyakar ƙarfin hali, 30kana kuma miƙo hannunka kana warkarwa, ana kuma yin mu'ujizai da abubuwan al'ajabi albarkacin sunan Baranka mai tsarki Yesu.” 31Bayan sun yi addu'a, wurin da suke a tattare ya raurawa. Sai duk aka cika su da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta faɗar maganar Allah gabagaɗi.
32To, duk taron da suka ba da gaskiya kuwa nufinsu ɗaya ne, ra'ayinsu ɗaya, ba kuma waninsu da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, sai dai kome nasu ne baki ɗaya. 33Manzanni kuma suka yi shaida da tabbatarwa mai ƙarfi a kan tashin Ubangiji Yesu daga matattu. Alheri mai yawa yana tare da kowannensu, 34har ba wanda yake da rashi a cikinsu ko ɗaya, don duk masu gonaki ko gidaje sun sayar da su, 35sun kawo kuɗin, sun ajiye gaban manzanni, an kuwa rarraba wa kowa gwargwadon bukatarsa. 36Ana cikin haka sai Yusufu, wani Balawiye, asalinsa mutumin tsibirin Kubrus, wanda manzannin suke kira Barnaba, (wato ɗan ƙarfafa zuciya), 37ya sayar da wata gonarsa, ya kawo kuɗin ya ajiye a gaban manzannin.
1Amma wani mutum mai suna Hananiya, da matarsa Safiratu, ya sayar da wata mallakarsa, 2sai ya ɓoye wani abu daga cikin kuɗin, da sanin matarsa, ya kawo sashin kuɗin kurum ya ajiye a gaban manzanni. 3Sai Bitrus ya ce, “Kai, Hananiya, ta ƙaƙa Shaiɗan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki ƙarya, ka kuma ɓoye wani abu daga kuɗin gonar? 4Kafin ka sayar, ba taka ba ce? Bayan ka sayar kuma, kuɗin ba halalinka ba ne? Ta ƙaƙa ka riya wannan aiki a zuciyarka? Ai, ba mutum ka yi wa ƙarya ba, Allah ka yi wa.” 5Da jin wannan magana Hananiya ya fāɗi ya mutu. Duk waɗanda suka ji kuwa, matsanancin tsoro ya kama su. 6Samari suka taso, suka sa shi a likkafani, suka ɗauke shi suka fitar da shi, suka je suka binne shi.
7Bayan misalin sa'a uku matarsa ta shigo, ba da sanin abin da ya faru ba. 8Sai Bitrus ya ce mata, “Gaya mini, shin, haka kuka sayar da gonar nan?” Sai ta ce, “I, haka ne.” 9Amma Bitrus ya ce mata, “Ƙaƙa kuka gama baki ku gwada Ruhun Ubangiji? Kin ji tafiyar waɗanda suka binne mijinki, har sun iso bakin ƙofa ma, za su kuwa ɗauke ki, su fitar da ke.” 10Nan tāke, ta fāɗi a gabansa, ta mutu. Da dai samarin suka shigo, suka iske ta matacciya, suka ɗauke ta suka fitar da ita, suka binne ta a jikin mijinta. 11Sai matsanancin tsoro ya kama dukan ikilisiyar, da kuma dukan waɗanda suka ji labarin waɗannan abubuwa.
12To, an yi mu'ujizai da abubuwan al'ajabi masu yawa a cikin mutane ta hannun manzanni. Dukansu kuwa da nufi ɗaya sukan taru a Shirayin Sulemanu. 13Amma a cikin sauran mutane ba wanda ya yi ƙarfin halin shiga cikinsu, duk da haka kuwa jama'a suna girmama su. 14Masu ba da gaskiya sai ƙaruwa suke ta yi ga Ubangiji fiye da dā, jama'a masu yawan gaske mata da maza. 15Har ma ya kai ga fitowa da marasa lafiya tafarku, suna shimfiɗa su a kan gadaje da tabarmi, don in Bitrus ya zo wucewa, ko da inuwarsa ma ta bi ta kan waɗansunsu. 16Mutane kuwa suka yi ta taruwa daga garuruwan da suke kewayen Urushalima, suna ta kawo marasa lafiya da waɗanda baƙaƙen aljannu suke wahalshe su, dukansu kuwa aka warkar da su.
17Amma babban firist ya taso, da duk waɗanda suke tare da shi, wato 'yan ɗariƙa Sadukiyawa, suna kishi gaya, 18suka kama manzannin, suka sa su kurkuku. 19Amma da daddare sai wani mala'ikan Ubangiji ya buɗe ƙofofin kurkukun, ya fito da su, ya ce, 20“Ku tafi, ku tsaya a cikin Haikali, ku sanar da jama'a duk maganar wannan rai.” 21Da suka ji haka, suka shiga Haikalin da sassafe, suna koyarwa. To, babban firist ya fito, shi da waɗanda suke tare da shi, suka kira majalisa, da dukan shugabannin Isra'ilawa, suka aika zuwa kurkuku a kawo su. 22Amma da dogaran Haikali suka je, ba su same su a kurkukun ba, suka dawo suka ba da labari, suka ce, 23“Mun iske kurkukun a kulle sosai, masu tsaro kuma suna tsaro a bakin ƙofofin, amma da muka buɗe, sai muka tarar ba kowa a ciki.” 24To, da shugaban dogaran Haikali da manyan firistocin suka ji haka, suka ruɗe ƙwarai a game da su, suka rasa inda abin zai kai. 25Sai wani ya zo ya ce musu, “Ai, ga shi, mutanen nan da kuka sa a kurkuku suna nan a tsaye a Haikali, suna koya wa jama'a.” 26Sai shugaban dogaran Haikali da dogaran suka je suka kawo manzannin, amma fa ba ƙarfi da yaji ba, don suna tsoro kada jama'a su jejjefe su da duwatsu.
27Da suka kawo su, suka tsai da su a gaban majalisar. Sai babban firist ya tambaye su, 28ya ce, “Mun fa kwaɓe ku da gaske kada ku ƙara koyarwa da sunan nan, amma ga shi, kun gama Urushalima da koyarwarku, har ma kuna nema ku ɗafa mana alhakin jinin mutumin nan.” 29Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, “Wajibi ne mu yi wa Allah biyayya fiye da mutum. 30Allahn kakanninmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe ta wurin kafe shi a jikin gungume. 31Shi ne Allah ya ɗaukaka ga damansa, Shugaba da kuma Mai Ceto, domin ya buɗe wa Isra'ila hanyar tuba, su kuma sami gafarar zunubansu. 32Mu kuwa shaidu ne ga waɗannan al'amura, haka kuma Ruhu Mai Tsarki, wanda Allah ya bai wa masu yi masa biyayya.”
33Da suka ji haka, sai suka husata ƙwarai da gaske, suna so su kashe su. 34Amma wani Bafarisiye, mai suna Gamaliyal, masanin Attaura, wanda duk jama'a suke girmamawa, ya miƙe a cikin majalisa, ya yi umarni a fitar da mutanen nan a waje tukuna. 35Sa'an nan ya ce musu, “Ya ku 'yan'uwa Isra'ilawa, ku kula fa da abin da kuke niyyar yi wa mutanen nan. 36A shekarun baya wani mutum ya ɓullo, mai suna Tudas, wanda ya mai da kansa wani abu, wajen mutum arbaminya kuma suka bi shi, amma aka kashe ƙi, mabiyansa kuwa aka watsa su, suka lalace. 37A bayansa kuma, a lokacin ƙirgen mutane, wani mai sunan Yahuza Bagalile ya ɓullo, ya zuga waɗansu suka yi tawaye, suka bi shi. Shi ma ya hallaka, duk mabiyansa ma aka warwatsa su. 38To, a yanzu ma, ina gaya muku, ku fita daga sha'anin mutanen nan, ku ƙyale su. Idan dai niyyarsu ko aikinsu na mutum ne, ai, zai rushe, 39amma in na Allah ne, ba dama ku rushe su. Kada fa a same ku kuna gāba da Allah.”
40Sai suka bi shawararsa, suka kuma kirawo manzannin, suka yi musu dūka, suka kwaɓe su kada su ƙara magana da sunan Yesu, sa'an nan suka sake su. 41To, sai suka tashi daga gaban majalisar, suna farin ciki a kan an ga sun isa su sha wulakanci saboda sunan Yesu. 42Kowace rana kuwa, ko a Haikali ko a gida, ba su daina koyarwa da yin bishara, cewa Yesu shi ne Almasihu ba.
1To, a kwanakin nan da yawan masu bi yake Ƙaruwa, sai Yahudawa masu jin Helenanci suka yi wa Ibraniyawa gunaguni domin ba a kula da matansu gwauraye ba, a wajen rabon gudunmawa a kowace rana. 2Sai goma sha biyun nan suka kirawo duk jama'ar masu bi, suka ce, “Ai, bai kyautu ba mu mu bar wa'azin Maganar Allah, mu shagala a kan sha'anin abinci. 3Saboda haka, 'yan'uwa, sai ku zaɓi mutum bakwai daga cikinku, waɗanda ake yabawa, cike da Ruhu da kuma hikima, waɗanda za mu danƙa wa wannan aiki. 4Mu kuwa sai mu nace da yin addu'a da kuma koyar da Maganar.” 5Abin da suka faɗa kuwa ya ƙayatar da jama'a duka. Sai suka zaɓi Istifanas, mutumin da yake cike da bangaskiya da Ruhu Mai Tsarki, da Filibus, da Burokoras, da Nikanar, da Timan, da Barminas, da Nikolas mutumin Antakiya wanda dā ya shiga Yahudanci. 6Waɗannan ne aka gabatar a gaban manzannin. Bayan sun yi addu'a kuma, suka ɗora musu hannu.
7Maganar Allah kuwa sai ƙara haɓaka take yi, yawan masu bi kuma a birnin Urushalima sai ta ƙaruwa yake yi ƙwarai da gaske, firistoci masu yawan gaske kuma suka yi na'am da bangaskiyar nan.
8To, Istifanas, a cike da alheri da iko, ya yi ta yin manyan al'ajabai da mu'ujizai a cikin jama'a. 9Sa'an nan waɗansu na majami'ar da ake kira majami'ar Libartinawa, wato Kuraniyawa da Iskandariyawa, da kuma waɗansu daga ƙasar Kilikiya da ta Asiya, suka tasar wa Istifanas da muhawwara. 10Amma ko kaɗan ba dama su yi masa mūsu, domin ya yi magana da hikima, Ruhu yana iza shi. 11Sai suka zuga mutane a asirce, su kuwa suka ce, “Mun ji shi yana zagin Musa, yana saɓon Allah.” 12Ta haka suka ta da hankalin jama'a, da shugabanni, da malaman Attaura, su kuma suka aukar masa, suka kama shi, suka kawo shi a gaban majalisa. 13Sai suka gabatar da masu shaidar zur, suka ce, “Mutumin nan ba ya rabuwa da kushe tsattsarkan wurin nan, da kuma Attaura, 14don mun ji shi yana cewa, wannan Yesu Banazare zai rushe wurin nan, yă kuma sauya al'adun da Musa ya bar mana.” 15Da duk waɗanda suke zaune a majalisar suka zura masa ido, suka ga fuskarsa kamar fuskar mala'ika take.
1Sai babban firist ya ce, “Ashe, haka ne?” 2Sai Istifanas ya ce, “Ya ku 'yan'uwa da shugabanni, ku saurare ni. Allah Maɗaukaki ya bayyana ga kakanmu Ibrahim, sa'ad da yake ƙasar Bagadaza, tun bai zauna a Haran ba, 3ya ce masa, “‘Tashi daga ƙasarku, kuma daga cikin 'yan'uwanka, ka je ƙasar da zan nuna maka.” 4Sai ya tashi daga ƙasar Kaldiyawa, ya zauna a Haran. Daga can kuma, bayan mutuwar mahaifinsa, Allah ya kawo shi ƙasar nan da yanzu kuke zaune. 5Amma kuwa shi da kansa, bai ba shi gādonta ba, ko da tăki ɗaya, sai dai ya yi masa alkawari zai mallakar masa ita, shi da zuriyar bayansa, ko da yake ba shi da ɗa a lokacin. 6Abin da Allah ya faɗa kuwa shi ne zuriyar Ibrahim za su yi baƙunci a wata ƙasa, mutanen ƙasar kuwa za su bautar da su, su kuma gwada musu azaba har shekara arbaminya. 7“‘Har wa yau kuma,” Allah ya ce, “‘Al'ummar da za su bauta wa, ni zan hukunta ta, bayan haka kuma za su fito su bauta mini a wannan wuri.” 8Ya kuma yi masa alkawari a game da kaciya. Ta haka, da Ibrahim ya haifi Ishaku, ya yi masa kaciya a rana ta takwas. Ishaku ya haifi Yakubu, Yakubu kuma ya haifi kakanninmu goma sha biyun nan.
9“Kakannin nan namu kuwa, da yake suna kishin Yusufu, suka sayar da shi, aka kai shi Masar. Amma Allah yana tare da shi, 10ya kuma tsamo shi daga dukan wahalarsa, ya ba shi farin jini da hikima a gun Fir'auna, Sarkin Masar, shi kuwa ya naɗa shi mai mulkin Masar, ya kuma danƙa masa jama'ar gidansa duka. 11To, sai wata yunwa ta auku a dukan ƙasar Masar da ta Kan'ana, a game da matsananciyar wahala, har kakanninmu suka rasa abinci. 12Amma da Yakubu ya ji akwai alkama a Masar, ya aiki kakanninmu tafiyar farko. 13A tafiyarsu ta biyu Yusufu ya sanar da kansa ga 'yan'uwansa, asalinsa kuma ya sanu ga Fir'auna. 14Sai Yusufu ya aika wa mahaifinsa Yakubu yă zo, da kuma dukan 'yan'uwansa, mutum saba'in da biyar. 15Sai Yakubu ya tafi Masar. A can ma ya mutu, shi da kakanninmu. 16Sai aka ɗebo su aka mai da su Shekem, aka sa su a kabarin da Ibrahim ya saya da kuɗi azurfa a wurin 'ya'yan Hamor a nan Shekem.
17“Amma da lokacin cikar alkawarin da Allah ya yi wa Ibrahim ya gabato, jama'ar suka ƙaru, suka yawaita ƙwarai a ƙasar Masar, 18har aka yi wani sarki a Masar, wanda bai san ko wane ne Yusufu ba. 19Wannan sarki kuwa ya cuci kabilarmu, yana gwada wa kakanninmu azaba, yana sawa a yar da jariransu, don kada su rayu. 20A lokacin nan ne aka haifi Musa, yaro kyakkyawan gaske. Sai aka rene shi wata uku a gidan mahaifinsa. 21Da aka fitar da shi waje, 'yar Fir'auna ta ɗauke shi tallafinta, ta goya shi kamar ɗanta. 22Sai aka karantar da Musa a cikin dukan ilimin Masarawa, shi kuwa mutum mai iko ne a cikin magana da ayyukansa.
23“Yana gab da cika shekara arba'in ke nan, sai ya faɗo masa a rai yă ziyarci 'yan'uwansa Isra'ilawa. 24Da ya ga ana cutar ɗayansu, sai ya tăre wanda ake wulakantawa, ya rama masa, ya buge Bamasaren, ya mutu. 25Ya zaci 'yan'uwansa sun gane ta hannunsa ne Allah zai cece su. Amma ba su gane ba. 26Kashegari kuma waɗansu suna faɗa, sai ya nemi shirya su, ya ce, “‘Ku jama'a, ku 'yan'uwa ne fa, don me kuke cutar juna?” 27Amma mai cutar ɗan'uwa nasa sai ya ture Musa, ya ce, “‘Wa ya sa ka shugaba da alƙali a kanmu? 28Wato kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe Bamasaren nan na jiya?” 29Da jin wannan magana, sai Musa ya gudu ya yi baƙunci a ƙasar Madayana, a inda ya haifi 'ya'ya biyu maza.
30“To, bayan shekara arba'in, sai mala'ika ya bayyana a gare shi a cikin harshen wuta, a wani kurmi a jejin Dutsen Sina'i. 31Da Musa ya ga haka, ya yi mamakin abin da ya gani. Da ya matso domin ya duba, sai ya ji muryar Ubangiji tana cewa, 32“‘Ni ne Allahn kakanninka, Allahn Ibrahim da Ishaku da Yakubu.” Sai jikin Musa ya ɗauki rawa, bai kuma iya ƙarfin halin dubawa ba. 33Sai Ubangiji ya ce masa, “‘Tuɓe takalminka, domin wurin da kake tsayen nan, tsattsarka ne. 34Hakika, na ga wulakancin da ake yi wa mutanena da suke Masar, na ji nishinsu, na kuma sauko don in cece su. To, a yanzu sai ka zo in aike ka Masar.”
35“To, shi Musan nan da suka ƙi, suna cewa, “‘Wa ya sa ka shugaba da kuma alƙali?” Shi ne Allah ya aiko ya zama shugaba, da mai ceto, ta taimakon mala'ikan nan da ya bayyana a gare shi a cikin kurmin nan. 36Shi ne kuwa ya fito da su, bayan ya yi abubuwan al'ajabi da mu'ujizai a ƙasar Masar, da Bahar Maliya, da kuma a cikin jeji, har shekara arba'in. 37Wannan shi ne Musan da ya ce wa Isra'ilawa, “‘Allah zai tasar muku da wani annabi daga cikin 'yan'uwanku, kamar yadda ya tashe ni.” 38Shi ne kuma wanda yake a cikin ikilisiyar nan a jeji tare da mala'ikan da ya yi masa magana a Dutsen Sinai, tare da kakanninmu kuma. Shi ne kuma ya karɓo rayayyiyar magana domin ya kawo mana. 39Amma kakanninmu suka ƙi yi masa biyayya, suka ture shi, zuciyarsu ta koma ƙasar Masar. 40Suka ce wa Haruna, “‘Ka yi mana gumakan da za su yi mana jagaba, don Musan nan kam, da ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya auku a gare shi ba.” 41A lokacin nan suka ƙera ɗan maraƙi, suka yanka wa gunkin nan hadaya, suka riƙa farin ciki da aikin da suka yi da hannunsu. 42Saboda haka Allah ya juya musu baya, ya sallame su ga bautar taurari, yadda yake a rubuce a littafin annabawa cewa, “‘Ya ku jama'ar Isra'ila, Ni ne kuka yanka wa dabbobi, kuka miƙa wa hadaya, Har shekara arba'in a cikin jeji? 43Ai, yawo kuka yi da alfarwar Molek, Da surar tauraron gunki Ramfan, Wato surorin nan da kuka ƙera don ku yi musu sujada. Ni kuwa zan kawar da ku a can bayan Babila.”
44“Dā kakanninmu suna da alfarwar shaida a jeji, irin wadda mai maganar nan da Musa ya umarta a yi, daidai fasalin da ya gani. 45Alfarwar nan ita ce kakanninmu suka gāda, suka kuma kawo ƙasar nan a zamanin Joshuwa, bayan sun mallake ƙasar al'umman da Allah ya kora a gaban idonsu. Alfarwar nan kuwa tana nan har ya zuwa zamanin Dawuda, 46wanda ya sami tagomashi wurin Allah, har ya nemi alfarmar yi wa Allahn Yakubu masujada. 47Amma Sulemanu ne ya yi wa Allah gini. 48Duk da haka Maɗaukaki ba ya zama a gidaje, ginin mutum. Yadda Annabi Ishaya ya ce, 49“‘Allah ya ce, Sama ita ce kursiyina, Ƙasa kuwa matashin ƙafata. Wane wuri kuma za ku gina mini? Ko kuwa wane wuri ne wurin hutuna? 50Ba da ikona na halicci dukan waɗannan abubuwa ba?”
51“Ku kangararru, masu ɓatan basira, masu kunnen ƙashi, kullum kuna yi wa Ruhu Mai Tsarki tsayayya. Yadda kakanninku suka yi, haka ku ma kuke yi. 52A cikin annabawa wane ne kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun kuma kashe waɗanda suka yi făɗi a kan zuwan Mai Adalcin nan, wanda a yanzu kuka zama maciya amanarsa, da kuma makasansa, 53ku ne kuwa kuka karɓi Shari'a ta wurin mala'iku, amma ba ku kiyaye ta ba!”
54Da suka ji haka, suka husata ƙwarai da gaske, har suka ciji leɓe don jin haushinsa. 55Amma Istifanas, a cike da Ruhu Mai Tsarki, sai ya zuba ido sama, ya ga ɗaukakar Allah, da kuma Yesu yana tsaye a dama ga Allah. 56Sai ya ce, “Ga shi, ina ganin sama a buɗe, da kuma Ɗan Mutum a tsaye a dama ga Allah.” 57Amma suka ɗauki ihu ƙwarai, suka tattoshe kunnuwansu, suka aukar masa da nufi ɗaya, 58suka fitar da shi a bayan gari ya ta jifansa da dutse. Shaidu kuwa suka ajiye tufafinsu wurin wani saurayi, mai suna Shawulu. 59Suna ta jifan Istifanas, shi kuwa yana ta addu'a, yana cewa, “Ya Ubangiji Yesu, ka karɓi ruhuna.” 60Sa'an nan ya durƙusa, ya ɗaga murya da ƙarfi, ya ce, “Ya Ubangiji, kada ka ɗora musu wannan zunubi.” Da faɗar haka sai ya yi barci.
1Shawulu kuwa yana goyon bayan kisan Istifanas.
A ran nan kuwa wani babban tsanani ya auko wa ikilisiyar da take Urushalima. Duk aka warwatsa su a lardin Yahudiya da na Samariya, sai dai manzannin kawai. 2Sai waɗansu mutane masu bautar Allah suka binne Istifanas, suka yi masa kuka ƙwarai. 3Amma Shawulu ya yi ta yi wa Ikilisiya ɓarna ƙwarai da gaske, yana shiga gida gida, yana jan mata da maza, yana jefa su a kurkuku.
4To, waɗanda aka warwatsar ɗin kuwa, suka yi ta zazzagawa suna yin bishara. 5Filibus ya tafi birnin Samariya, yana ta yi musu wa'azin Almasihu. 6Da taron suka ji, suka kuma ga mu'ujizan da Filibus yake yi, da nufi ɗaya suka mai da hankali ga abin da ya faɗa. 7Domin da yawa masu baƙaƙen aljannu suka rabu da su, aljannun kuwa suna ta ihu. Shanyayyu da guragu da yawa kuma an warkar da su. 8Saboda haka aka yi ta farin ciki a garin ƙwarai da gaske.
9Akwai wani mutum kuwa, mai suna Saminu, wanda dā yake sihiri a birnin, har yana ba Samariyawa mamaki, yana cewa shi wani muhimmi ne. 10Duk jama'a kuwa mai da hankali a gare shi, babba da yaro, suna cewa, “Mutumin nan, ai, ikon nan ne na Allah, da ake kira mai girma.” 11Sai suka mai da hankali a gare shi, don ya daɗe yana ta ba su al'ajabi da sihirinsa. 12Amma da suka gaskata bisharar da Filibus ya yi a kan Mulkin Allah, da kuma sunan Yesu Almasihu, duka aka yi musu baftisma mata da maza. 13Har Saminu da kansa ma ya ba da gaskiya, bayan an yi masa baftisma kuma ya manne wa Filibus. Ganin kuma ana yin mu'ujizai da manyan al'ajibai, ya yi mamaki ƙwarai.
14To, da manzannin da suke Urushalima suka ji Samariyawa sun yi na'am da Maganar Allah, suka aika musu da Bitrus da Yahaya. 15Su kuwa sa suka iso, suka yi musu addu'a don su sami Ruhu Mai Tsarki, 16domin bai sauko wa ko wannensu ba tukuna, sai dai kawai an yi musu baftisma ne da sunan Ubangiji Yesu. 17Sai suka ɗora musu hannu, suka kuwa sami Ruhu Mai Tsarki.
18To, da Saminu ya ga, ashe, ta ɗora hannun manzanni ne ake ba da Ruhun, sai ya miƙa musu kuɗi, 19ya ce, “Ni ma ku ba ni wannan iko, don kowa na ɗora wa hannu, yă sami Ruhu Mai Tsarki.” 20Amma Bitrus ya ce masa, “Ku hallaka, kai da kuɗinka, don ka zaci da kuɗi ne za ka sami baiwar Allah! 21Ba ruwanka da wannan al'amari sam, don zuciyarka ba ɗaya take ba a gaban Allah. 22Saboda haka sai ka tuba da wannan mugun aiki naka, ka roƙi Ubangiji ko a gafarta maka abin da ka riya a zuciyarka. 23Domin na ga kai tushen ɗaci ne, kana kulle a cikin mugunta.” 24Sai saminu ya amsa ya ce, “Ku roƙar mini Ubangiji kada ko ɗaya daga cikin abin da kuka faɗa ya aukar mini.”
25To, bayan manzannin sun tabbatar da Maganar Ubangiji, sun faɗe ta, suka koma Urushalima, suna yin bishara a ƙauyukan Samariyawa da yawa.
26Sai mala'ikan Ubangiji ya ce wa Filibus, “Tashi, ka yi kudu, ka bi hanyar da ta fito daga Urushalima zuwa Gaza,” wato hanyar hamada. 27Sai ya tashi ya tafi. Ga wani mutumin Habasha, wani bābā, mai babban matsayi a mulkin Kandakatu, sarauniyar Habasha, shi ne kuwa ma'ajinta, ya zo Urushalima ne yin sujada, 28yana komawa gida a zaune a cikin keken dokinsa, yana karatun littafin Annabi Ishaya. 29Sai Ruhu ya ce wa Filibus, “Matsa ka yi kusa da keken dokin nan.” 30Sai Filibus ya yi gudu zuwa wurinsa, ya ji shi yana karatun littafin Annabi Ishaya. Ya ce, “Kana kuwa fahimtar abin da kake karantawa?” 31Sai ya ce, “Ina fa? Sai ko wani ya fassara mini.” Sai ya roƙi Filibus ya hau su zauna tare. 32Wannan kuwa shi ne nassin da yake karantawa, “An ja shi kamar tunkiya zuwa mayanka. Kamar yadda ɗan rago yake shiru a hannun mai sausayarsa, Haka, ko bakinsa bai buɗe ba. 33An yi masa ƙasƙanci har an hana masa gaskiyarsa. Wa yake iya ba da labarin zamaninsa? Domin an katse ransa daga duniya.”
34Sai bābān ya ce wa Filibus, “Shin kam, annabin nan, maganar wa yake yi? Tasa ko ta wani?” 35Sai Filibus ya buɗe baki ya fara da wannan Nassi, yana yi masa bisharar Yesu. 36Suna cikin tafiya, suka iso wani ruwa, sai bābān ya ce, “Ka ga ruwa! Me zai hana a yi mini baftisma?” 37Filibus ya ce, “In dai ka ba da gaskiya da zuciya ɗaya, ai, sai a yi maka.” Bābān ya amsa ya ce, “Na gaskata Yesu Almasihu ɗan Allah ne.” 38Sai ya yi umarni a tsai da keken dokin. Sai dukansu biyu suka gangara zuwa cikin ruwan, Filibus da bābān, ya yi masa baftisma. 39Da suka fito daga ruwan, Ruhun Ubangiji ya fyauce Filibus, bābān kuma bai ƙara ganinsa ba. Sai ya yi ta tafiya yana farin ciki. 40Amma aka ga Filibus a Azotus. Sai ya zaga dukan garuruwa, yana yin bishara, har ya isa Kaisariya.
(A. M. 22.6-16; 26.12-18)
1Shawulu kuwa yana kan tsananta yin kashedi da gāba da masu bin Ubangiji, cewa zai kashe su, sai ya je wurin babban firist, 2ya roƙe shi ya yi masa wasiƙu zuwa majami'un Dimashƙu, don in ya sami musu bin wannan hanya, mata ko maza, yă zo da su birnin Urushalima a ɗaure. 3Yana tafiya ke nan, ya yi kusa da Dimashƙu, ba zato sai ga wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi. 4Sai ya fāɗi, ya kuma ji wata murya tana ce masa, “Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?” 5Shi kuma ya ce, “Wane ne kai, ya Ubangiji?” Sai ya ce, “Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa. 6Amma ka tashi ka shiga gari, a can za a faɗa maka abin da za ka yi.” 7Abokan tafiyarsa kuwa suka rasa bakin magana, suna jin muryar, amma ba su ga kowa ba. 8Sai Shawulu ya tashi, amma da ya buɗe ido sai ya kasa gani. Sai da aka yi masa jagora, aka kai shi Dimashƙu. 9Kwanansa uku ba ya gani, ba ya kuma ci, ba ya sha.
10To, akwai wani mai bi a Dimashƙu, mai suna Hananiya. Ubangiji ya yi masa magana a cikin wahayi ya ce, “Hananiya.” Shi kuwa ya ce, “Na'am, ya Ubangiji.” 11Sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka tafi hanyar nan da ake kira Miƙaƙƙiya, ka yi tambaya a gidan Yahuza, ko akwai wani mutumin Tarsus, mai suna Shawulu, ga shi nan, yana addu'a, 12har ma a cikin wahayi ya ga wani mutum, mai suna Hananiya, ya shigo ya ɗora masa hannu, don ya sāke samun ganin gari.” 13Amma Hananiya ya amsa ya ce, “Ya Ubangiji, na sha jin labarin mutumin nan a gun mutane da yawa, a kan yawan muguntar da ya yi wa tsarkakanka a Urushalima. 14Ga shi kuma manyan firistoci sun ba shi izini ya ɗaure duk mai yin addu'a da sunanka har a nan ma.” 15Amma Ubangiji ya ce masa, “Kai dai, je ka, domin shi ma'aikacina ne zaɓaɓɓe, domin yă sanar da sunana ga al'ummai, da sarakuna, da kuma Isra'ilawa. 16Domin zan sanar da shi yawan wuyar da lalle zai sha saboda sunana.” 17Sai Hananiya ya tafi, ya shiga gidan. Da ya ɗora masa hannu, sai ya ce, “Ya ɗan'uwana Shawulu, Ubangiji ne ya aiko ni, wato Yesu, wanda ya bayyana a gare ka a kan hanyar da ka biyo, domin ka sāke gani, a kuma cika ka da Ruhu Mai Tsarki.” 18A nan take sai wani abu kamar ɓawo ya faɗo daga idanunsa, sai ya sāke gani. Sa'an nan ya tashi, aka yi masa baftisma. 19Sai ya ci abinci, ƙarfinsa kuma ya komo.
Shawulu kuwa ya yi 'yan kwanaki tare da masu bi da suke Dimashƙu. 20Nan da nan ya fara wa'azin Yesu a majami'unsu, cewa shi ne Ɗan Allah. 21Duk waɗanda suka ji shi, suka yi ta al'ajabi, suka ce, “Ashe, ba wannan ne ya watsa masu yin addu'a da sunan nan a Urushalima ba? Ya zo nan ne ma da niyyar ya kai su a gaban manyan firistoci a ɗaure.” 22Sai Shawulu ya ƙara ƙarfafa, yana ta dama hankalin Yahudawan da suke zaune a Dimashƙu, yana tabbatarwa, cewa Yesu shi ne Almasihu.
23Bayan an ɗan daɗe Yahudawa suka ƙulla shawara su kashe shi. 24Amma Shawulu ya sami labarin makircinsu. Dare da rana suna fako a ƙofofin gari don su kashe shi, 25amma da daddare almajiransa suka tafi da shi, suka zura shi ta wata taga a jikin garu cikin babban kwando.
26Da ya zo Urushalima ya yi ƙoƙarin shiga a cikin masu bi, amma duk suka ji tsoronsa, don ba su gaskata shi mai bi ba ne. 27Amma Barnaba ya kama hannunsa ya kai shi wurin manzannin, ya gaya musu yadda Shawulu ya ga Ubangiji a hanya, da yadda Ubangiji ya yi masa magana, da kuma yadda ya yi wa'azi gabagaɗi da sunan Yesu a Dimashƙu. 28A daga nan ya yi ta cuɗanya da su a Urushalima, 29yana wa'azi gabagaɗi da sunan Ubangiji. Ya kuma riƙa yin magana da Yahudawa masu jin Helenanci, yana muhawwara da su, amma suka yi ta neman hanyar kashe shi. 30Da 'yan'uwa suka fahimci haka, suka kawo shi Kaisariya, suka aika da shi Tarsus.
31Sa'an nan ne Ikilisiyar duk ƙasar Yahudiya, da ta Galili, da ta Samariya ta sami lafiya, ta ingantu sosai, suna tafiyar da al'amuransu da tsoron Ubangiji, Ruhu Mai Tsarki yana taimakonsu, har suka yawaita.
32To, da Bitrus ya zazzaga lardi duka, sai kuma ya je wurin tsarkakan nan da suke zaune a Lidda. 33A nan ya tarar da wani mutum, mai suna Iniyasu, wanda yake kwance a kan gado shekara takwas, yana shanyayye. 34Sai Bitrus ya ce masa, “Iniyasu, Yesu Almasihu ya warkar da kai. Tashi ka kintsa gadonka.” A nan tāke ya tashi. 35Duk mutanen Lidda da na ƙasar Sarona kuwa suka gan shi, suka juyo ga Ubangiji.
36A Yafa kuwa akwai wata mai bi, mai suna Tabita, wato Dokas ke nan. Matar nan kuwa lazimar aiki nagari ce, da kuma gudunmawa. 37A lokacin nan ta yi rashin lafiya, ta mutu. Da suka yi mata wanka, suka shimfiɗe ta a kan bene. 38Da yake Lidda kusa da yafa take, da masu bi suka ji Bitrus yana can, suka aiki mutum biyu wurinsa, su roƙe shi ya zo wurinsu ba da jinkiri ba. 39Sai Bitrus ya tashi ya tafi tare da su. Da ya iso suka kai shi benen. Dukan mata gwauraye suka tsaya kusa da shi, suna kuka, suna nunnuna riguna da tufafi da Dokas ta yi musu tun suna tare. 40Amma Bitrus ya fitar da su duka waje, ya durƙusa, ya yi addu'a. Ya juya wajen gawar, ya ce, “Tabita, tashi.” Ta buɗe ido, da ta ga Bitrus, sai ta tashi zaune. 41Ya kuwa miƙa mata hannu ya tashe ta. Sai ya kira tsarkaka da mata gwauraye, ya miƙa musu ita rayayyiya. 42Labari ya bazu a dukan Yafa, mutane da yawa kuwa suka gaskata da Ubangiji. 43To, ya zauna kwanaki da yawa a Yafa a gidan wani majemi mai suna Saminu.
1An yi wani mutum a Kaisariya, mai suna Karniliyas, wani jarumi ne na ƙungiyar soja da ake kira Ƙungiyar Italiya. 2Shi kuwa mutum ne mai ibada, yana tsoron Allah shi da iyalinsa duka, yana yi wa Yahudawa gudunmawa hannu sake, yana kuma addu'a ga Allah a kai a kai. 3Wata rana wajen ƙarfe uku na yamma, ya ga wani mala'ikan Allah a fili cikin wahayi, ya shigo, ya ce masa, “Ya Karniliyas.” 4Shi kuwa ya zura masa ido a tsorace, ya ce, “Ya Ubangiji, mene ne?” Mala'ikan kuma ya ce masa, “Addu'arka da sadakarka sun kai har a gaban Allah, abubuwan tunawa ne kuma a gare shi. 5To, a yanzu, sai ka aiki mutane Yafa su kirawo Saminu, wanda ake kira Bitrus, 6ya sauka a gun Saminu majemi, wanda gidansa yake a bakin bahar.” 7Da mala'ikan da ya yi masa magana ya tafi, ya kira barorinsa biyu, da kuma wani soja mai ibada daga cikin waɗanda suke yi masa hidima kullum. 8Da ya ba su labarin kome, ya aike su Yafa.
9Kashegari suna cikin tafiya, sun zo kusa da gari ke nan, sai Bitrus ya hau kan soro yin addu'a, wajen rana tsaka. 10Yunwa ta kama shi, har ya so ya ci wani abu. Ana cikin shirya abincin, sai wahayi ya zo masa, 11ya ga sama ta dare, wani abu kuma yana saukowa kamar babban mayafi, ana zuro shi ƙasa ta kusurwoyinsa huɗu. 12A cikinsa akwai kowace irin dabba, da masu jan ciki, da tsuntsaye. 13Sai ya ji wata murya ta ce masa, “Bitrus, tashi, ka yanka ka ci.” 14Amma Bitrus ya ce, “A'a, ya Ubangiji, don ban taɓa cin wani abu marar tsarki ko mai ƙazanta ba.” 15Sai ya sāke jin murya, ji na biyu, ta ce, “Abin da Allah ya tsarkake, kada ka ce da shi marar tsarki.” 16Da aka yi wannan sau uku, nan da nan aka yi sama da abin.
17Bitrus na a cikin damuwa ƙwarai a kan ko mece ce ma'anar wahayin da aka yi masa, sai ga mutanen da Karniliyas ya aiko a tsaye a ƙofar zaure, sun riga sun tambayi gidan Saminu, 18suna sallama, suna tambaya ko Saminu da ake kira Bitrus a nan ya sauka. 19Tun Bitrus yana bibiya wahayin nan, Ruhu ya ce masa, “Ga mutum uku nan suna nemanka. 20Tashi, ka sauka, ku tafi tare, ba da wata shakka ba, domin ni ne na aiko su.” 21Sai Bitrus ya sauka a wurin mutanen, ya ce musu, “Ga ni, ni ne kuke nema. Wace magana take tafe da ku?” 22Sai suka ce, “Wani jarumi ne, mai suna Karniliyas, mutumin kirki, mai tsoron Allah, wanda duk jama'ar Yahudawa suke yabo, shi ne wani tsattsarkan mala'ika ya umarce shi, ya aiko ka je gidansa, ya ji maganarka.” 23Sai Bitrus ya shigo da su, ya sauke su. Kashegari ya tashi suka tafi tare, waɗansu 'yan'uwa kuma daga Yafa suka raka shi. 24Kashegari kuma suka shiga Kaisariya. Dā ma Karniliyas yana tsammaninsu, har ya gayyato 'yan'uwansa da aminansa. 25Bitrus yana shiga gidan ke nan sai Karniliyas ya tarye shi, ya fāɗi a gabansa, ya yi masa sujada. 26Amma Bitrus ya tashe shi, ya ce, “Tashi, ai, ni ma ɗan adam ne.” 27Bitrus yana zance da shi, ya shiga ya tarar mutane da yawa sun taru. 28Ya ce musu, “Ku da kanku kun sani, bai halatta Bayahude ya yi cuɗanya, ko ya ziyarci wani na wata kabila dabam ba. Amma Allah ya nuna mini kada in ce da kowa marar tsarki, ko mai ƙazanta. 29Saboda haka da aka neme ni, na zo, ban ce a'a ba. To, a yanzu ina so in ji abin da ya sa kuka kira ni.”
30Sai Karniliyas ya ce, “Yau kwana uku ke nan, a wajen war haka, ina addu'ar ƙarfe uku na yamma a gidana, sai wani mutum a tsaye a gabana, yana saye da tufafi masu ɗaukar ido, 31ya ce, “‘Ya Karniliyas, an amsa addu'arka sadakarka kuma ta zama abar tunawa ga Allah. 32Saboda haka sai ka aika Yafa a kirawo Saminu, wanda ake kira Bitrus, yă sauka a gidan Saminu majemi a bakin bahar.” 33Nan da nan kuwa na aika maka, ka kuma kyauta da ka zo. To, a yanzu ga mu duk mun hallara a gaban Allah, domin mu ji duk irin abin da Ubangiji ya umarce ka.”
34Sai Bitrus ya kāda baki ya ce, “Hakika na gane lalle Allah ba ya tara, 35amma a kowace al'umma duk mai tsoronsa, mai kuma aikata adalci, abin karɓuwa ne a gare shi. 36Allah ya aiko wa Isra'ilawa, ana yi musu bisharar salama ta wurin Yesu Almasihu, shi ne kuwa Ubangijin kowa. 37Kun dai san labarin nan da ya bazu a duk ƙasar Yahudiya, an fara tun daga ƙasar Galili, bayan baftismar da Yahaya ya yi wa'azi, 38wato labarin Yesu Banazare, yadda Allah ya shafe shi da Ruhu Mai Tsarki da kuma iko, da yadda ya riƙa zagawa yana aikin alheri, yana warkar da duk waɗanda Iblis ya matsa wa, domin Allah yana tare da shi. 39Mu kuwa shaidu ne ga duk abin da ya yi a ƙasar Yahudawa da Urushalima. Shi ne kuma suka kashe ta wurin kafa shi a jikin gungume. 40Shi ne Allah ya tashe shi a rana ta uku, ya kuma yarda ya bayyana, 41ba ga dukan jama'a ba, sai dai ga shaidun nan da Allah ya zaɓa tun dā, wato mu ke nan, da muka ci muka sha tare da shi, bayan ya tashi daga matattu. 42Ya kuma umarce mu mu yi wa mutane wa'azi, mu kuma tabbatar cewa shi ne wanda Allah ya sa mai hukunta rayayyu da matattu. 43Shi ne duk annabawa suka yi wa shaida, cewa albarkacin sunansa duk mai gaskatawa da shi zai sami gafarar zunubai.”
44Bitrus yana a cikin wannan magana, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauko wa dukan masu jinta. 45Sai Yahudawa masu bi, ɗaukacin waɗanda suka zo tare da Bitrus, suka yi mamakin ganin har al'ummai ma an zubo musu baiwar Ruhu Mai Tsarki. 46Domin sun ji suna magana da waɗansu harsuna, suna ta ɗaukaka Allah. Sa'an nan Bitrus ya ce, 47“Akwai mai iya hana ruwan da za a yi wa mutanen nan baftisma, waɗanda suka sami Ruhu Mai Tsarki, kamar yadda mu ma muka samu?” 48Sai ya yi umarni a yi musu baftisma da sunan Yesu Almasihu. Sa'an nan suka roƙe shi ya ƙara 'yan kwanaki a gunsu.
1To, manzanni da 'yan'uwa da suke a ƙasar Yahudiya suka ji, cewa al'ummai ma sun yi na'am da Maganar Allah. 2Da Bitrus ya zo Urushalima, 'yan ɗariƙar masu kaciyar nan suka yi masa sūka, 3suka ce, “Ga shi, ka shiga wurin marasa kaciya, har ka ci abinci tare da su!” 4Sai Bitrus ya fara, yana yi musu bayani bi da bi cewa, 5“Ni dai, ina birnin Yafa ina addu'a, sai wahayi ya zo mini, na ga wani abu yana saukowa kamar babban mayafi, an zuro shi daga sama ta kusurwoyinsa huɗu, har ya zo wurina. 6Da na zuba masa ido, na duba na ga dabbobi, da namomin jeji, da masu jan ciki, da kuma tsuntsaye a ciki. 7Sai kuma na ji wata murya ta ce mini, “‘Bitrus, ka tashi, ka yanka, ka ci.” 8Amma na ce, “‘A'a, ya Ubangiji, don ba wani abu marar tsarki ko mai ƙazanta da ya taɓa shiga bakina.” 9Sai muryar ta amsa daga Sama ta yi magana ta biyu, ta ce, “‘Abin da Allah ya tsarkake, kada ka ce da shi marar tsarki.” 10An yi wannan sau uku, sa'an nan aka janye abin sama. 11Ba zato sai ga mutum uku a tsaye a ƙofar gidan da muke, an aiko su wurina ne daga Kaisariya. 12Sai Ruhu ya ce mini in tafi tare da su, ba tare da wata shakka ba. 'Yan'uwan nan shida kuma suka rako ni, har muka shiga gidan mutumin nan. 13Sai ya gaya mana yadda ya ga mala'ika a tsaye a gidansa, yana cewa, “‘Ka aika Yafa a kirawo Saminu, wanda ake kira Bitrus, 14shi zai faɗa maka maganar da za ka sami ceto a game da ita, kai da jama'ar gidanka duka.” 15Da fara maganata, Ruhu Mai Tsarki ya sauko musu, a daidai yadda ya sauko mana tun da farko. 16Sai na tuna da Maganar Ubangiji, yadda ya ce, “‘Yahaya kam, da ruwa ya yi baftisma, amma ku da Ruhu Mai Tsarki za a yi muku baftisma.” 17Tun da yake Allah ya yi musu baiwa daidai da wadda ya yi mana, sa'ad da muka gaskata da Ubangiji Yesu Almasihu, wane ni da zan dage wa Allah!” 18Da suka ji haka, suka rasa ta cewa, suka kuma ɗaukaka Allah suka ce, “Ashe, har al'ummai ma Allah ya ba su tuba zuwa rai.”
19To, waɗanda suka warwatsu saboda tsananin nan da ya tashi a kan sha'anin Istifanas, sun yi tafiya har ƙasar Finikiya, da tsibirin Kubrus, da birnin Antakiya, ba su yin wa'azin Maganar Allah ga kowa sai ga Yahudawa kaɗai. 20Amma akwai waɗansu mutanen Kubrus da na Kurane a cikinsu waɗanda da isowarsu Antakiya suka yi wa al'ummai magana, suna yi musu bisharar Ubangiji Yesu. 21Ikon Ubangiji kuwa na tare da su, har mutane da yawa da suka ba da gaskiya suka juyo ga Ubangiji. 22Sai labarin nan ya kai kunnen ikilisiyar da take Urushalima, Ikilisiyar kuma ta aiki Barnaba zuwa can Antakiya. 23Da ya iso ya kuma ga alherin da Allah ya yi musu, ya yi farin ciki, ya gargaɗe su duka su tsaya ga Ubangiji da dukan zuciyarsu, 24domin shi mutum ne nagari a cike da Ruhu Mai Tsarki da bangaskiya. Sai mutane masu yawan gaske suka ƙaru ga Ubangiji. 25Sai Barnaba ya tafi Tarsus neman Shawulu, 26bayan da ya same shi kuwa, sai ya kawo shi Antakiya. Shekara gaba ɗaya cur suna taruwa da Ikilisiya, suna koya wa mutane masu yawan gaske. A Antakiya ne aka fara kiran masu bi da suna Kirista.
27To, a kwanakin nan waɗansu annabawa suka zo Antakiya daga Urushalima. 28Sai ɗaya daga cikinsu, mai suna Agabas, ya miƙe a tsaye, ya yi faɗi da ikon Ruhu, cewa za a yi wata babbar yunwa, a duniya duka, an yi ta kuwa a zamanin Kalaudiyas. 29Sai masu bi suka ɗaura niyya, kowa gwargwadon ƙarfinsa, su aika wa yan'uwan da suke ƙasar Yahudiya gudunmawa. 30Haka kuwa suka yi, suka aika wa dattawan Ikilisiya ta hannun Barnaba da Shawulu.
1A lokacin nan kuwa sarki Hirudus ya fara gwada wa waɗansu 'yan Ikilisiya azaba, 2har ma ya sare Yakubu ɗan'uwan Yahaya da takobi. 3Da ya ga abin ya ƙayatar da Yahudawa, har wa yau kuma ya kama Bitrus, shi ma. A kwanakin idin abinci marar yisti ne kuwa. 4Da ya kama shi, ya sa shi a kurkuku, ya danƙa shi a hannun soja hurhuɗu kashi huɗu, don su yi tsaronsa, da niyyar kawo shi a gaban jama'a bayan idin. 5Sai aka tsare Bitrus a kurkuku, Ikilisiya kuwa ta himmantu ga roƙon Allah saboda shi.
6A daren da in gari ya waye Hirudus yake da niyyar fito da shi a yi masa hukunci, Bitrus kuwa yana barci a tsakanin soja biyu, ɗaure da sarƙa biyu, masu tsaronsa kuma suna bakin ƙofa suna tsaron kurkukun, 7sai ga mala'ikan Ubangiji a tsaye a kusa da shi, wani haske kuma ya haskaka ɗakin, sa'an nan mala'ikan ya bugi Bitrus a kwiɓi, ya tashe shi, ya ce, “Maza, ka tashi.” Sai kuwa sarƙar ta zube daga hannunsa. 8Mala'ikan ya ce masa, “Yi ɗamara, ka sa takalminka.” Sai ya yi. Sai ya ce masa, “Yafa mayafinka, ka biyo ni.” 9Sai ya fito ya bi shi, bai san abin da mala'ikan nan ya yi hakika ne ba, cewa yake wahayi ake yi masa. 10Da suka wuce masu tsaron farko da na biyu, suka isa ƙyauren ƙarfe na ƙofar shiga gari, ƙyauren kuwa ya buɗe musu don kansa. Sai suka fita. Sun ƙure wani hanya ke nan, nan da nan sai mala'ikan ya bar shi. 11Da Bitrus ya koma a cikin hankalinsa, ya ce, “Yanzu kam na tabbata, Ubangiji ne ya aiko mala'ikansa, ya cece ni daga hannun Hirudus, da kuma dukan mugun fatan Yahudawa.”
12Da ya gane haka, ya je gidan Maryamu, mahaifiyar Yahaya wanda ake kira Markus, a inda aka taru da yawa, ana addu'a. 13Da ya ƙwanƙwasa ƙofar zauren, wata baranya mai suna Roda ta zo ji ko wane ne. 14Da ta shaida muryar Bitrus, ba ta buɗe ƙofar ba don murna, sai ta koma ciki a guje, ta ce Bitrus yana tsaye a ƙofar zaure. 15Sai suka ce mata, “Ke dai akwai ruɗaɗɗiya.” Ita kuwa ta nace a kan shi ne. Su kuwa suka ce, “To, mala'ikansa ne!” 16Bitrus dai ya ta ƙwanƙwasawa, da suka buɗe suka gan shi, suka yi ta al'ajabi. 17Shi kuwa ya ɗaga musu hannu su yi shiru, ya kuma bayyana musu yadda Ubangiji ya fito da shi daga kurkuku. Ya kuma ce, “Ku faɗa wa Yakubu da 'yan'uwa waɗannan abubuwa.” Sa'an nan ya tashi ya tafi wani wuri.
18Da gari ya waye kuwa ba ƙaramar rigima ce ta tashi a tsakanin sojan nan ba, a kan abin da ya sami Bitrus. 19Da Hirudus ya neme shi bai same shi ba, ya yi tuhumar masu tsaron, ya kuma yi umarni a kashe su. Sa'an nan ya tashi daga ƙasar Yahudiya ya tafi Kaisariya, ya yi 'yan kwanaki a can.
20To, sai Hirudus ya yi fushi ƙwarai da mutanen Taya da na Sidon. Suka zo wurinsa da nufi ɗaya. Bayan da suka rinjayi Bilastasa, sarkin fāda, suka nemi zaman lafiya, domin ga ƙasar sarkin nan suka dogara saboda abincinsu. 21Ana nan a wata rana da aka shirya, Hirudus ya yi shigar sarauta, ya zauna a gadon sarauta, ya yi musu jawabi. 22Taron mutane kuwa suka ɗauki sowa, suna cewa, “Kai! ka ji muryar wani Allah, ba ta mutum ba!” 23Nan tāke sai mala'ikan Ubangiji ya buge shi don bai ɗaukaka Allah ba. Sai tsutsotsi suka yi ta cinsa har ya mutu.
24Maganar Allah kuwa sai ƙara haɓaka take yi, tana yaɗuwa.
25Sai Barnaba da Shawulu suka komo daga Urushalima, bayan sun cika aikin da aka yi musu, suka kuma zo da Yahaya wanda ake kira Markus.
1To, a Ikilisiyar da ke Antakiya akwai waɗansu annabawa, da masu koyarwa, wato Barnaba, da Saminu wanda ake kira Băƙi, da Lukiyas Bakurane, da Manayan wanda aka goya tare da sarki Hirudus, da kuma Shawulu. 2Sa'ad da suke yi wa Ubangiji ibada, suna kuma yin azumi, sai Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Sai ku kuɓe mini Barnaba da Shawulu domin aikin da na kira su a kai.” 3Bayan kuma sun yi azumi, sun kuma yi addu'a, sai suka ɗora musu hannu, suka sallame su.
4Su kuwa, da Ruhu Mai Tsarki ya aike su, suka tafi Salukiya, daga can kuma suka shiga jirgin ruwa, sai tsibirin Kubrus. 5Da suka kai Salamis, suka sanar da Maganar Allah a majami'un Yahudawa, ga kuma Yahaya yana taimakonsu. 6Bayan sun zazzaga tsibirin duka har Bafusa, suka iske wani mai sihiri, annabin ƙarya, Bayahude, mai suna Bar-yashu'a, 7Wanda yake tare da muƙaddas Sarjiyas Bulus, mutum ne mai basira. Sai muƙaddashin ya kira Barnaba da Shawulu ya nemi jin Maganar Allah. 8Amma Alimas mai sihirin nan, (don wannan ita ce ma'anar sunansa), ya mūsa musu, yana neman bauɗar da muƙaddashin nan daga bangaskiya. 9Shawulu kuwa, wanda kuma ake kira Bulus, a cike da Ruhu Mai Tsarki, ya zuba masa ido, 10ya ce, “Kai babban maha'inci, munafiƙi, ɗan Iblis, magabcin adalci duka, ba za ka daina karkata miƙaƙƙun hanyoyin Ubangiji ba? 11To, ga shi, hannun Ubangiji yana kanka, za ka makance, ba za ka ga rana ba har wani lokaci.” A nan take kuwa sai wani hazo da duhu suka rufe shi, ya yi ta neman wanda zai yi masa jagora. 12Da muƙaddashin ya ga abin da ya faru, sai ya ba da gaskiya, yana mamaki da koyarwar Ubangiji.
13Sai Bulus da abokan tafiyarsa suka tashi daga Bafusa a jirgin ruwa, suka isa Bariyata ta ƙasar Bamfiliya. Yahaya kuwa ya bar su, ya koma Urushalima. 14Amma suka wuce gaba daga Bariyata, suka tafi Antakiya ta ƙasar Bisidiya. A ran Asabar kuma sai suka shiga majami'a suka zauna. 15Bayan da aka yi karatun Attaura da littattafan annabawa, shugabannin majami'ar suka aika musu, suka ce, “'Yan'uwa, in kuna da wata maganar gargaɗi da za ku yi wa jama'a, sai ku yi.” 16Sai Bulus ya miƙe, ya ɗaga hannu a yi shiru, ya ce, “Ya ku 'yan'uwa Isra'ilawa, da sauran masu tsoron Allah, ku saurara! 17Allahn jama'ar nan Isra'ila ya zaɓi kakanninmu, ya ɗaukaka jama'ar sa'ad da suke baƙunci a ƙasar Masar, da maɗaukakin iko kuma ya fito da su daga cikinta. 18Har wajen shekara arba'in yake haƙuri da su a cikin jeji. 19Ya kuma hallaka al'umma bakwai a ƙasar Kan'ana, sai ya raba musu ƙasar tasu gādo, suka zauna har shekara arbaminya da hamsin. 20Bayan haka kuma, sai ya naɗa musu mahukunta har ya zuwa zamanin Annabi Sama'ila. 21Sa'an nan suka roƙa a naɗa musu sarki, sai Allah ya ba su Saul ɗan Kish, mutumin kabilar Biliyaminu, har shekara arba'in. 22Bayan da ya kawar da shi sai ya gabatar da Dawuda ya zama sarkinsu, ya kuma shaide shi da cewa, “‘Na sami Dawuda ɗan Yesse, mutum ne da nake ƙauna ƙwarai, wanda zai aikata dukan nufina.” 23Daga zuriyar mutumin nan ne Allah ya kawo wa Isra'ila Mai Ceto, Yesu kamar yadda ya yi alkawari. 24Kafin ya bayyana a fili kuwa, Yahaya ya yi wa duk jama'ar Isra'ila wa'azi cewa, su tuba a kuma yi musu baftisma. 25Yayin da Yahaya ya kusa gama nasa zamani, sai ya ce, “‘Wa kuke tsammani nake? Ba fa ni ne shi ɗin nan ba. Amma ga shi akwai wani mai zuwa a bayana, wanda ko takalmansa ma ban isa in ƙwance ba.”
26“Ya ku 'yan'uwa, zuriyar Ibrahim, da kuma sauran masu tsoron Allah a cikinku, mu fa aka aiko wa kalmar ceton nan. 27Ga shi, mazaunan Urushalima da shugabanninsu ba su gane shi ba, sa'an nan kuma ba su fahimci maganar annabawa da ake karantawa a kowace Asabar ba, har suka cika maganar nan ta annabawa, a yayin da suka hukunta shi. 28Ko da yake ba su same shi da wani laifin kisa ba, duk da haka suka roƙi Bilatus don a kashe shi. 29Da suka cikasa dukkan abin da aka rubuta a game da shi, suka sauko da shi daga kan gungumen, suka sa shi a kabari. 30Amma Allah ya tashe shi daga matattu. 31Kwanaki da yawa kuwa yana bayyana ga waɗanda suka zo tare da shi Urushalima daga Galili, waɗanda a yanzu su ne shaidunsa ga jama'a. 32Mu ma mun kawo muku albishir, cewa, alkawarin nan da Allah ya yi wa kakanninmu, 33ya cika mana shi, mu zuriyarsu, da ya ta da Yesu daga matattu, yadda yake a rubuce a cikin Zabura ta biyu cewa, “‘Kai Ɗana ne, Ni Ubanka ne yau.” 34A game da ta da shi daga matattu da Allah ya yi, a kan cewa ba zai sāke komawa cikin halin ruɓa ba kuwa, ga abin da ya ce, “‘Zan yi muku tsattsarkar albarkar nan da na tabbatar wa Dawuda.” 35Domin a wata Zabura ma ya ce, “‘Ba za ka yarda Mai Tsarkinka ya ruɓa ba.” 36Dawuda kam, bayan da ya bauta wa mutanen zamaninsa bisa ga nufin Allah, ya yi barci, aka binne shi tare da kakanninsa, ya kuwa ruɓe. 37Amma shi wannan da Allah ya tashe shi, bai ruɓa ba. 38Saboda haka, 'yan'uwa, sai ku sani albarkacin mutumin nan ne ake sanar da ku gafarar zunubanku. 39Ta gare shi kuma, duk masu ba da gaskiya suka kuɓuta daga dukan abubuwan da ba dama Shari'ar Musa ta kuɓutar da ku. 40Saboda haka sai ku mai da hankali, kada abin nan da littattafan annabawa ke faɗa ya aukar muku, wato 41“‘Ga shi, ku masu rainako, Za ku ruɗe don mamaki, ku shuɗe! Domin zan yi wani aiki a zamaninku, Aikin da ba yadda za a yi ku gaskata, Ko da wani ya gaya muku.”
42Suna fita daga majami'a ke nan, sai mutane suka roƙe su, don su ƙara yi musu wannan magana a ran Asabar mai zuwa. 43Da jama'a suka watse, Yahudawa da yawa, da kuma waɗanda suka shiga Yahudanci, masu ibada, suka bi Bulus da Barnaba. Su kuma suka yi musu magana, suna yi musu gargaɗi cewa su zauna a cikin alherin Allah.
44Da Asabar ta kewayo, kusan duk birnin, suka hallara don su ji Maganar Allah. 45Amma da Yahudawa suka ga taro masu yawa, suka yi kishi gaya, suka yi ta musun abubuwan da Bulus ya faɗa, suna zaginsa. 46Sai Bulus da Barnaba suka yi magana gabagaɗi, suka ce, “Ku, ya wajaba a fara yi wa Maganar Allah, amma da yake kun ture ta, kun nuna ba ku cancanci samun rai madawwami ba, to, za mu juya ga al'ummai. 47Domin haka ubangiji ya umarce mu, ya ce, “‘Na sa ka haske ga al'ummai, Don ka zama sanadin ceto, har ya zuwa iyakar duniya.”
48Da al'ummai suka ji haka, suka yi farin ciki, suka ɗaukaka Maganar Ubangiji, ɗaukacin kuma waɗanda aka ƙaddara wa samun rai madawwami suka ba da gaskiya. 49Maganar Ubangiji kuwa, sai ta yi ta yaɗuwa a duk ƙasar. 50Amma Yahudawa suka zuga waɗansu mata masu ibada, masu daraja, da kuma waɗansu manyan gari, suka haddasa tsanani ga Bulus da Barnaba, suka kore su daga ƙasarsu. 51Su kuwa suka karkaɗe ƙurar ƙafafunsu don shaida a kansu, suka tafi Ikoniya. 52Amma kuwa masu bi suna ta farin ciki matuƙa, suna kuma a cike da Ruhu Mai Tsarki.
1To, a Ikoniya suka shiga majami'ar Yahudawa tare, suka yi wa'azi, har mutane masu yawa, Yahudawa da al'ummai, suka ba da gaskiya. 2Amma Yahudawa da suka ƙi bi, suka zuga al'ummai, suka ɓata tsakaninsu da 'yan'uwa. 3Sai Bulus da Barnaba suka daɗe a nan ƙwarai, suna wa'azi gabagaɗi bisa ga ikon Ubangiji, shi da ya shaida maganar alherinsa ta yarjin mu'ujizai da abubuwan al'ajabi ta hannunsu. 4Amma mutanen birni suka rarrabu, waɗansu suka koma bayan Yahudawa, waɗansu kuma bayan manzannin. 5Sa'ad da al'ummai da Yahudawa tare da shugabanninsu suka tasar wa manzannin, su wulakanta su, su jejjefe su da duwatsu, 6suka sami labari, suka gudu zuwa biranen Likoniya wato Listira da Darba, da kuma kewayensu. 7A nan suka yi ta yin bisharar.
8To, a Listira akwai wani mutum a zaune, wanda ƙafafunsa ba su da ƙarfi, gurgu ne tun da aka haife shi, bai ma taɓa tafiya ba. 9Yana sauraron wa'azin Bulus, sai Bulus ya zuba masa ido, da ya ga bangaskiyarsa ta isa a warkar da shi, 10sai ya ɗaga murya ya ce, “Tashi, ka tsaya cir.” Sai wuf ya zabura, har ya yi tafiya. 11Da taron suka ga abin da Bulus ya yi, suka ɗaga murya gaba ɗaya suna cewa da Likoniyanci, “Lalle, alloli sun sauko mana da siffar mutane!” 12Sai suka ce Barnaba shi ne Zafsa, Bulus kuwa don shi ne shugaban magana, shi ne Hamisa. 13Sai sarkin tsafin Zafsa, wanda ɗakin gunkinsa yake a ƙofar gari, ya kawo bajimai da tutocin furanni a ƙofar gari, yana son yin hadaya tare da jama'a. 14Amma da manzannin nan, Barnaba da Bulus, suka ji haka, suka kyakketa tufafinsu, suka ruga zuwa cikin taron, suna ɗaga murya suna cewa, 15“Don me kuke yin haka? Ai, mu ma 'yan adam ne kamarku, mun dai kawo muku bishara ne, domin ku juya wa abubuwan banzan nan baya, ku juyo ga Allah Rayayye, wanda ya halicci sama, da ƙasa, teku, da kuma dukkan abin da yake a cikinsu. 16Shi ne a zamanin dā, ya bar dukan al'ummai su yi yadda suka ga dama. 17Duk da haka kuwa bai taɓa barin kansa, ba shaida ba, domin yana yin alheri, shi da yake yi muku ruwan sama, da damuna mai albarka, yana ƙosar da ku da abinci, yana kuma faranta muku rai.” 18Duk da waɗannan maganganu da ƙyar suka hana jama'ar nan yin hadaya saboda su.
19Amma waɗansu Yahudawa suka zo daga Antakiya da Ikoniya, da suka rarrashi taron, suka jejjefe Bulus suka ja shi zuwa bayan gari, suna zato ya mutu. 20Amma da masu bi suka taru a kansa, sai ya tashi ya koma garin. Kashegari kuma ta tafi Darba tare da Barnaba. 21Bayan sun yi bishara a wannan gari, sun kuma sami masu bi da yawa, suka koma Listira da Ikoniya, da kuma Antakiya, 22suna ƙarfafa masu bi, suna yi musu gargaɗi su tsaya ga bangaskiya, suna cewa, sai da shan wuya mai yawa za mu shiga Mulkin Allah. 23Bayan kuma sun zaɓar musu dattawa a kowace Ikilisiya, a game da addu'a da azumi, suka danƙa su ga Ubangiji, wanda dā ma suka gaskata da shi.
24Da suka zazzaga ƙasar Bisidiya, suka isa ƙasar Bamfiliya. 25Da kuma suka faɗi Maganar a Bariyata, suka tafi Ataliya. 26Daga nan kuma suka shiga jirgin ruwa sai Antakiya, a inda tun dā aka yi musu addu'a alherin Allah ya kiyaye su a cikin aikin nan da a yanzu suka gama. 27Da suka iso, suka tara jama'ar Ikilisiya suka ba da labarin dukan abin da Allah ya aikata ta wurinsu, da kuma yadda ya buɗe wa al'ummai ƙofar bangaskiya. 28Sun kuwa jima a can tare da masu bi.
1Sai kuma waɗansu mutane suka zo daga Yahudiya suna koya wa 'yan'uwa, suna cewa, “In ba an yi muku kaciya kamar yadda al'adar Musa take ba, ba dama ku sami ceto.” 2A kan wannan magana kuwa ba ƙaramar gardama da muhawwara Bulus da Barnaba suka sha yi da mutanen ba. Sai aka sa Bulus da Barnaba da kuma waɗansunsu, su je Urushalima a gun manzanni da dattawan ikilisiya a kan wannan magana kuwa. 3To, da Ikilisiya ta raka su, sai suka zazzaga ƙasar Finikiya da ta Samariya, suna ba da labarin tubar al'ummai, sun kuwa ƙayatar da dukan 'yan'uwa ƙwarai. 4Da suka isa Urushalima, Ikilisiya, da manzanni, da dattawan Ikilisiya suka yi musu maraba, su kuma suka gaggaya musu dukan abin da Allah ya yi ta wurinsu. 5Amma waɗansu masu ba da gaskiya, 'yan ɗariƙar Farisiyawa, suka miƙe, suka ce, “Wajibi ne a yi musu kaciya, a kuma umarce su, su bi Shari'ar Musa.”
6Sai manzannin da dattawan Ikilisiya suka taru don su duba maganar. 7Bayan da aka yi ta muhawwara da gaske, Bitrus ya miƙe a tsaye, ya ce musu, “Ya 'yan'uwa, kun sani tun farkon al'amari, Allah ya yi zaɓe a cikinku, cewa dai ta bakina ne al'ummai za su ji maganar bishara, su ba da gaskiya. 8Allah kuwa, masanin zuciyar kowa, ya yi musu shaida da ya ba su Ruhu Mai Tsarki, kamar yadda ya ba mu. 9Bai kuma nuna wani bambanci a tsakaninmu da su ba, tun da yake ya tsarkake zukatansu saboda bangaskiyarsu. 10Saboda haka, don me kuke gwada Allah, ta ɗora wa almajiran nan kayan da mu, duk da kakanninmu, muka kasa ɗauka? 11Amma mun gaskata, cewa, albarkacin alherin Ubangiji Yesu ne muka sami ceto, kamar yadda su ma suka samu.” 12Sai duk taron mutane suka yi tsit, suka saurari Barnaba da Bulus, sa'ad da suke ba da labarin mu'ujizai da abubuwan al'ajabi, da Allah ya yi ga al'ummai ta wurinsu.
13Bayan da suka gama jawabi, sai Yakubu ya amsa ya ce, “Ya ku 'yan'uwa, ku saurare ni. 14Bitrus ya ba da labari yadda Allah ya fara kula da al'ummai, domin ya keɓe wata jama'a daga cikinsu ta zama tasa. 15Wannan kuwa daidai yake da maganar annabawa, yadda yake a rubuce cewa, 16“‘Bayan haka kuma zan komo, In sāke gina gidan Dawuda da ya rushe, In sāke ta da kangonsa, In tsai da shi, 17Domin sauran mutane su nemi Ubangiji, Wato al'umman da suke nawa.” 18Haka Ubangiji ya ce, shi da ya bayyana waɗannan abubuwa tun zamanin dā. 19Saboda haka, a ganina, kada mu matsa wa al'ummai waɗanda suke juyowa ga Allah, 20sai dai mu rubuta musu wasiƙa, su guji abubuwan ƙazanta na game da gumaka, da fasikanci, da cin abin da aka maƙure, da kuma cin nama tare da jini. 21Domin tun a zamanin dā, a kowane gari akwai masu yin wa'azi da littattafan Musa, ana kuma karanta su a majami'u kowace Asabar.”
22Sai manzanni da dattawan Ikilisiya, tare da dukan 'yan Ikilisiya, suka ga ya kyautu su zaɓi waɗansu daga cikinsu, su aike su Antakiya tare da Bulus da Barnaba. Sai suka aiki Yahuza, wanda ake kira Barsaba, da kuma Sila, shugabanni ne a cikin 'yan'uwa, 23da wannan takarda cewa, “Daga 'yan'uwanku, manzanni da dattawan Ikilisiya, zuwa ga 'yan'uwanmu na al'ummai a Antakiya da ƙasar Suriya da ta Kilikiya. Gaisuwa mai yawa. 24Tun da muka sami labari, cewa waɗansu daga cikinmu sun ta da hankalinku da maganganu, suna ruɗa ku, ko da yake ba mu umarce su da haka ba, 25sai muka ga ya kyautu, da yake bakinmu ya zo ɗaya, mu aiko muku da waɗansu zaɓaɓɓun mutane, tare da ƙaunatattunmu Barnaba da Bulus, 26waɗanda suka sayar da ransu saboda sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu. 27Don haka, ga shi, mun aiko muku Yahuza da Sila, su ma za su gaya muku waɗannan abubuwa da bakinsu. 28Domin Ruhu Mai Tsarki ya ga ya kyautu, mu ma mun gani, kada a ɗora muku wani nauyi fiye da na waɗannan abubuwa da suke wajibi, wato 29ku guji abin da aka yanka wa gunki, da cin nama tare da jini, da cin abin da aka maƙure, da kuma fasikanci. In kun tsare kanku daga waɗannan, za ku zauna lafiya. Wassalam.”
30Su kuma da aka sallame su, suka tafi Antakiya, da suka tara jama'ar, suka ba da wasiƙar. 31Da suka karanta ta, suka yi farin ciki saboda gargaɗin. 32Yahuza da Sila kuma, da yake su annabawa ne, suka gargaɗi 'yan'uwa da maganganu masu yawa, suka kuma ƙarfafa su. 33Bayan da suka yi 'yan kwanaki a wurin, sai 'yan'uwa suka sallame su lafiya, suka koma wurin waɗanda suka aiko su.[ 34Amma Sila ya ga ya kyautu shi ya zauna a nan.] 35Bulus da Barnaba kuwa suka dakata a Antakiya, suna koyarwa suna kuma yin bisharar Maganar Ubangiji, tare da waɗansu ma da yawa.
36Da aka jima, sai Bulus ya ce wa Barnaba, “Bari yanzu mu koma mu dubo 'yan'uwa a kowane gari da muka sanar da Maganar Ubangiji, mu ga yadda suke.” 37Barnaba kuwa ya so su tafi da Yahaya, wanda ake kira Markus. 38Amma Bulus bai ga ya kyautu su tafi da wanda ya rabu da su a ƙasar Bamfiliya, ya ƙi tafiya aiki tare da su ba. 39Sai matsanancin saɓanin ra'ayi ya auku, har ya kai su ga rabuwa. Barnaba ya ɗauki Markus, suka shiga jirgin ruwa zuwa tsibirin Kubrus, 40amma Bulus ya zaɓi Sila, bayan da 'yan'uwa suka yi masa addu'a alherin Allah ya kiyaye shi, ya tafi. 41Bulus ya zazzaga ƙasar Suriya da ta Kilikiya, yana ta ƙarfafa Ikilisiyoyi.
1Sai kuma Bulus ya zo Darba da Listira. Akwai wani almajiri a Listira, mai suna Timoti, ɗan wata Bayahudiya mai bi, mahaifinsa kuwa Bahelene ne. 2Shi kuwa 'yan'uwa da suke Listira da Ikoniya na yabonsa. 3Sai Bulus ya so Timoti ya rako shi, har ya yi masa kaciya saboda Yahudawan da suke waɗannan wurare, don duk sun san mahaifinsa Bahelene ne. 4Lokacin da suke tafiya suna bin gari gari, suka riƙa gaya wa jama'a ka'idodin da manzanni da dattawan ikilisiya suka ƙulla a Urushalima, don su kiyaye su. 5Ta haka ikilisiyoyi suka ƙarfafa a cikin bangaskiya, a kowace rana suna ƙara yawa.
6Sai suka zazzaga ƙasar Firijiya da ta Galatiya, saboda Ruhu Mai Tsarki ya hana su yin Maganar Ubangiji a ƙasar Asiya. 7Da suka zo kan iyakar ƙasar Misiya, sai suka yi ƙoƙarin zuwa ƙasar Bitiniya, amma Ruhun Yesu bai yardar musu ba. 8Suka kuwa ratsa ƙasar Misiya, suka gangara zuwa Taruwasa. 9Wata rana da daddare aka yi wa Bulus wahayi, ya ga wani mutumin ƙasar Makidoniya yana tsaye, yana roƙonsa yana cewa, “Ka ƙetaro Makidoniya, ka taimake mu mana.” 10Da kuwa ya ga wahayin, nan tāke sai muka nemi tafiya Makidoniya, muka tabbata cewa Allah ne ya kira mu mu yi musu bishara.
11Shi ke nan fa, sai muka tashi a jirgin ruwa daga Taruwasa, muka miƙe sosai har zuwa tsibirin Samutaraki, kashegari kuma sai Niyabolis, 12daga nan kuma sai Filibi ta ƙasar Makidoniya, wadda take babbar alkarya ce a wannan waje, birnin Romawa ne kuma. A nan birnin muka yi 'yan kwanaki.
13A ran Asabar muka fita ƙofar gari, muka je bakin kogi, a inda muke tsammani akwai wurin addu'a. A nan muka zauna, muka yi wa matan da suka taru magana. 14Ɗaya daga cikin masu sauraronmu wata mace ce, mai suna Lidiya, mai sayar da jar hajja, mutuniyar Tayatira, mai ibada ce kuma. Ubangiji ya buɗe zuciyarta, har ta mai da hankali ga abin da Bulus ya faɗa. 15Da aka yi mata baftisma tare da jama'ar gidanta, ta roƙe mu ta ce, “Da yake kun amince ni mai ba da gaskiya ga Ubangiji ce, to, sai ku zo gidana ku sauka.” Sai ta rinjaye mu.
16Wata rana muna tafiya wurin yin addu'a, sai muka gamu da wata yarinya mai aljani mai duba, tana kuwa samo wa iyayengijinta amfani mai yawa ta wurin dubar. 17Sai ta riƙa binmu, mu da Bulus, tana ihu tana cewa, “Mutanen nan fa bayin Allah Maɗaukaki ne, suna kuwa sanar da ku hanyar ceto!” 18Haka ta dinga yi kwana da kwanaki, har Bulus ya ji haushi ƙwarai, ya juya ya ce wa aljanin, “Na umarce ka da sunan Yesu Almasihu, ka rabu da ita.” A nan tāke kuwa ya rabu da ita.
19Da iyayengijinta suka ga hanyar samunsu ta toshe, suka danƙe Bulus da Sila, suka ja su har zuwa bakin kasuwa gaban mahukunta. 20Da suka kai su a gaban alƙalai suka ce, “Mutanen nan suna birkita garinmu ƙwarai da gaske, Yahudawa ne kuwa. 21Suna kuma koyar da al'adun da ba su halatta mu karɓa ko mu bi ba, da yake mu Romawa ne.” 22Sai jama'a suka ɗungumo musu gaba ɗaya, alƙalan kuma suka yi kaca-kaca da tufafinsu, suka tuttuɓe su, suka yi umarni a bulale su da tsumagu. 23Da aka bulale su da gaske, aka jefa su a kurkuku, aka umarci yari ya tsare su da kyau. 24Shi kuwa da ya karɓi wannan umarni, sai ya jefa su a can ciki cikin kurkuku, ya sa su a turu.
25A wajen tsakar dare Bulus da Sila suna addu'a suna waƙoƙin yabon Allah, 'yan sarka kuwa suna sauraronsu, 26farat ɗaya, sai aka yi wata babbar rawar ƙasa, har harsashin ginin kurkuku ya raurawa. Nan da nan ƙofofin suka bubbuɗe, mărin kowa kuma ya ɓalle. 27Da yari ya farka daga barci ya ga ƙofofin kurkuku a buɗe, ya zaro takobinsa, yana shirin kashe kansa, cewa yake 'yan sarƙa sun gudu. 28Amma Bulus ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Kada ka cuci kanka, ai duk muna nan!” 29Sai yari ya ce a kawo fitilu, ya yi wuf ya ruga ciki, ya fāɗi gaban Bulus da Sila, yana rawar jiki don tsoro. 30Sa'an nan ya fito da su waje, ya ce, “Ya shugabanni, me zan yi in sami ceto?” 31Su kuwa suka ce, “Ka gaskata da Ubangiji Yesu, za ka sami ceto, kai da iyalinka.” 32Sa'an nan suka gaya masa Maganar Ubangiji, shi da iyalinsa duka. 33A nan tāke da daddaren nan ya ɗebe su, ya wanke musu raunukansu. Nan da nan kuwa aka yi masa baftisma da dukan iyalinsa. 34Sa'an nan ya kawo su gidansa, ya kawo musu abinci, ya yi ta farin ciki matuƙa, domin shi da iyalinsa duka sun gaskata da Allah.
35Amma da gari ya waye, sai alƙalan suka aiko dogari, suka ce, “Suka ce a sāke mutanen nan.” 36Yari kuwa ya shaida wa Bulus maganar, ya ce, “Alƙalai sun aiko a sake ku, saboda haka yanzu sai ku fito, ku tafi lafiya.” 37Amma Bulus ya ce musu, a “Ai, a fili suka daddoke mu, ba ko bin ba'asi, mu ma da muke Romawa bisa ga 'yangaranci, suka jefa mu a kurkuku, a yanzu kuma sā fitar da mu a ɓoye? Sai dai su zo da kansu su fito da mu.” 38Sai dogarai suka shaida wa alƙalan wannan magana. Su kuwa da suka ji Bulus da Sila Romawa ne suka tsorata. 39A sa'an nan sai suka zo suka tubar musu, bayan kuma sun fito da su, suka roƙe su su bar garin. 40To, da suka fita daga kurkukun, suka tafi wurin Lidiya. Bayan da sun ga 'yan'uwa, suka kuma ƙarfafa musu zuciya, suka tashi.
1To, da suka bi ta Amfibolis da Aboloniya, suka isa Tasalonika, a inda wata majami'ar Yahudawa tāke. 2Sai Bulus ya shiga a wurinsu kamar yadda ya saba, Asabar uku a jere yana muhawwara da su daga cikin Littattafai, 3yana yi musu bayani, yana kuma tabbatarwa, cewa lalle ne, Almasihu yă sha wuya, ya kuma tashi daga matattu. Ya kuma ce, “Yesun nan da nake sanar muku, shi ne Almasihu.” 4Sai waɗansunsu suka amince, suka koma wajen Bulus da Sila, haka kuma babban taron Helenawa masu ibada, da manyan mata ba kaɗan ba. 5Amma Yahudawa, saboda kishi, suka ɗibi waɗansu ashararai, 'yan iska, suka tara jama'a suka hargitsa garin kaf, suka fāɗa wa gidan Yason, suna nemansu don su fito da su a gaban taron jama'a. 6Da ba su same su ba, sai suka jawo Yason da waɗansu 'yan'uwa, har gaban mahukuntan garin, suna ihu suna cewa, “Mutanen nan masu ta da duniya a tsaye, ga su sun zo nan ma, 7har ma Yason ya sauke su! Dukansu kuwa suna saɓa dokokin Kaisar, suna cewa wani ne sarki, cewa shi Yesu ne.” 8Da mutanen gari da mahukunta suka ji wannan, hankalinsu ya tashi. 9Ba su sake su ba, sai da suka karɓi kuɗin lamuni a hannun Yason da sauransu.
10Nan da nan kuwa da dare ya yi, 'yan'uwa suka sallami Bulus da Sila su tafi biriya. Da suka isa can kuma suka shiga majami'ar Yahudawa. 11To, waɗannan Yahudawa kam, sun fi na Tasalonika dattaku, domin sun karɓi Maganar hannu biyu biyu, suna ta nazarin Littattafai a kowace rana, su ga ko abin haka yake. 12Saboda haka da yawa daga cikinsu suka ba da gaskiya, har waɗansu Helenawa ba kaɗan ba, mata masu daraja, da kuma maza. 13Amma da Yahudawan Tasalonika suka ji labari Bulus yana sanar da Maganar Allah a Biriya ma, suka je suka zuga taro masu yawa a can ma, suna ta da hankalinsu. 14Nan da nan kuwa 'yan'uwa suka tura Bulus a bakin bahar, amma Sila da Timoti suka dakata a nan. 15Waɗanda suka rako Bulus kuwa, sai da suka kai shi har Atina. Bayan da Bulus ya yi musu saƙon umarni zuwa wurin Sila da Timoti, cewa su zo wurinsa da gaggawa, suka tafi.
16To, sa'ad da Bulus yake dākonsu a Atina, ya ji haushi ƙwarai da ya ga a ko'ina gumaka ne a birnin. 17A kowace rana ya yi ta muhawwara a cikin majami'a da Yahudawa, da waɗansu masu ibada, da kuma waɗanda yake tararwa a bakin kasuwa. 18Har wa yau kuma waɗansu Abikuriyawa da Sitokiyawa masu ilimi suka ci karo da shi. Waɗansu suka ce, “Me wannan mai surutu yake nufi?” Waɗansu kuwa suka ce “Ga alama, mai yin wa'azin bāƙin alloli ne”ūdomin kawai yana yin bisharar Yesu, da kuma tashi daga matattu. 19Sai suka riƙe shi suka kai shi Tudun Arasa, suka ce, “Ko ka faɗa mana wace irin baƙuwar koyarwa ce wannan da kake yi? 20Domin ka kawo mana abin da yake baƙo a gare mu, muna kuwa so mu san ma'anarsa.” 21Alhali kuwa duk Atinawa da baƙinsu ba abin da suke yi, sai kashe zarafinsu a wajen jin baƙon abu, ko kuma ɗorar da shi.
22Sai Bulus ya miƙe a tsaye Tudun Arasa, ya ce, “Ya ku mutanen Atina, na dai lura, ku masoyan ibada ne ƙwarai, ta kowane fanni. 23Don sa'ad da nake zagawa, na duba abubuwan da kuke yi wa ibada, har ma na tarar da wani bagadin hadaya da wannan rubutu a sama da shi cewa, “‘Saboda Allahn da ba a sani ba.” To, shi wanda kuke yi wa sujada ba a tare da kun san shi ba, shi ina sanar muku. 24Allahn da ya halicci duniya da dukkan abin da yake cikinta, shi da yake Ubangijin sama da ƙasa, ba ya zama a haikalin ginin mutum. 25Haka kuma ba ya neman wani taimako daga gun mutum, sai ka ce wani abu yake bukata, tun da yake shi da kansa ne yake ba dukkan mutane rai, da numfashi, da dukkan abubuwa. 26Shi ne kuma ya halicci dukkan al'umma daga tsatso ɗaya, domin su zauna a dukan sararin duniya, ya kuma ƙayyade zamanansu da iyakokin ƙasashensu, 27wato nufinsa shi ne su neme shi, ko watakila sā laluba su same shi, alhali kuwa ba ya nesa da kowane ɗayanmu. 28Domin “‘Ta gare shi ne muke rayuwa, muke motsi, muka kuma kasance,” kamar yadda waɗansu mawaƙanku ma suka ce, “‘Hakika, mu ma zuriyarsa ce.” 29To, da yake mu zuriyar Allah ne, ai, bai kamata mu tsammaci Allah yana kama da wata surar zinariya, ko ta azurfa, ko ta dutse ba, wadda mutum ya ƙago ta dabararsa. 30A dā kam, Allah ya kawar da kai ga zamanin jahilci, amma a yanzu yana umartar dukkan mutane a ko'ina su tuba, 31tun da yake ya tsai da ranar da zai yi wa duniya shari'a, shari'a adalci, ta wurin mutumin nan da ya sa, wannan kuwa ya tabbatar wa dukan mutane, da ya tashe shi daga matattu.”
32Da dai suka ji maganar tashin matattu, sai waɗansu suka yi ba'a, amma waɗansu suka ce, “A game da wannan magana kam, mā sāke jin abin da za ka faɗa.” 33Sai Bulus ya fita daga cikinsu. 34Amma waɗansu mutane suka koma wajensa suka ba da gaskiya, a cikinsu har Diyonisiyas, ɗan majalisar Tudun Arasa, da wata mace mai suna Damarisa, da waɗansu dai haka.
1Bayan haka Bulus ya tashi daga Atina ya tafi Koranti. 2A can ya tarar da wani Bayahude mai suna Akila, asalinsa kuwa mutumin Fantas ne, bai daɗe da zuwa daga ƙasar Italiya ba, tare da matarsa Bilkisu, don Kalaudiyas ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya je wurinsu. 3Da yake kuma sana'arsu ɗaya ce, maɗinkan tanti ne, ya sauka a wurinsu, suka yi ta aiki tare. 4Ya kuma yi ta yin muhawwara a majami'a a kowace Asabar, yana ta rinjayar Yahudawa da al'ummai.
5Sa'ad da Sila da Timoti suka zo daga Makidoniya, Bulus ya dukufa a kan yin wa'azi, yana tabbatar wa Yahudawa, cewa Almasihu dai Yesu ne. 6Da suka mūsa masa, suna ta zaginsa, ya karkaɗe tufafinsa ya ce musu, “Alhakinku yana a wuyanku! Ni kam na fita. Daga yau wurin al'ummai zan je.” 7Sai ya tashi daga nan ya je gidan wani mutum mai suna Titus Yustus mai ibada, gidansa kuwa gab da majami'a yake. 8Sai Kirisbus, shugaban majami'ar ya ba da gaskiya ga Ubangiji, shi da jama'ar gidansa duka. Korantiyawa kuma da yawa da suka ji maganar Bulus suka ba da gaskiya, aka yi musu baftisma. 9Wata rana da daddare, Ubangiji ya yi wa Bulus wahayi, ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, sai dai ka yi ta wa'azi, kada ka yi shiru, 10domin ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa ka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.” 11Sai Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da wata shida, yana ta koyar da Maganar Allah a cikinsu.
12Amma sa'ad da Galiyo yake muƙaddashin ƙasar Akaya, Yahudawa suka tasar wa Bulus da nufi ɗaya suka kawo shi a gaban shari'a, 13suka ce, “Mutumin nan yana rarrashin mutane, don su bauta wa Allah ta hanyar da Shari'ar ta hana.” 14Bulus yana shirin yin magana ke nen sai Galiyo ya ce wa Yahudawan, “Ku Yahudawa! Da ma wani laifi ya yi, ko munafunci, da sai in iya sauraronku. 15Amma tun da yake gardama ce kawai a kan kalmomi, da sunaye, da kuma shari'arku, ai, sai ku ji da ita, ku da kanku. Ni kam, ba ni da niyyar yin shari'a irin waɗannan abubuwa.” 16Sai ya kore su daga ɗakin shari'a. 17Sai duk suka kama Sastanisu, shugaban majami'a, suka yi masa dūka a gaban gadon shari'a. Amma Galiyo ko yă kula.
18Bulus kuwa da ya ƙara kwanaki da yawa, bayan da ya sausaye kansa a Kankiriya don ya cika wa'adin da ya ɗauka, ya yi bankwana da 'yan'uwa, ya shiga jirgin ruwa zuwa ƙasar Suriya, tare da Bilikisu da Akila. 19Sai suka isa Afisa, a can ne kuma ya bar su, shi kuwa ya shiga majami'a ya yi muhawwara da Yahudawa. 20Sai suka roƙe shi ya ƙara jimawa a wurinsu, amma bai yarda ba. 21Sai dai ya yi bankwana da su, ya ce, “Zan dawo wurinku in Allah ya so.” Sa'an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa.
22Da ya sauka a Kaisariya, sai ya je Urushalima, don ya gaisa da ikilisiya, sa'an nan ya tafi Antakiya.
23Bayan da ya ɗan jima a nan, ya tashi ya zazzaga ƙasar Galatiya da ta Firijiya, yana bin gari gari, yana ƙarfafa dukan masu bi.
24To, wani Bayahude mai suna Afolos ya zo Afisa. Shi kuwa asalinsa mutumin Iskandariya ne, masani ne kuwa, ya san Littattafai ƙwarai da gaske. 25An karantar da shi a tafarkin Ubangiji, da yake kuma muhimmanci ne ƙwarai, yakan yi ta magana a kan al'amuran Yesu, yana kuma koyar da su sosai, amma fa baftismar Yahaya kaɗai ya sani. 26Sai ya fara wa'azi gabagaɗi a majami'a, amma da Bilkisu da Akila suka ji maganarsa, suka ja shi a jika, suka ƙara bayyana masa tafarkin Allah sosai da sosai. 27Da ya so hayewa zuwa ƙasar Akaya, 'yan'uwa suka taimake shi, suka rubuta wa masu bi wasiƙa su karɓe shi hannu biyu biyu. Da kuwa ya isa, ya yi matuƙar taimako ga waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin alherin Ubangiji, 28don yā kayar da Yahudawa ƙwarai a gaban jama'a, yana tabbatar musu ta wurin Littattafai cewa Almasihu dai Yesu ne.
1To, a lokacin da Afolos yake a Koranti, Bulus ya zazzaga ƙasar ta kan tudu, ya gangara zuwa Afisa. A can ya tarar da waɗansu masu bi, 2sai ya ce musu, “Kun sami Ruhu Mai Tsarki sa'ad da kuka ba da gaskiya?” Suka ce masa, “Ba mu ma ji zuwan Ruhu Mai Tsarki ba.” 3Sai ya ce, “To, wace baftisma ke nan aka yi muku?” Suka ce, “Irin ta Yahaya ce.” 4Bulus ya ce, “Ai, Yahaya baftisma ya yi a tuba, yana faɗa wa mutane su gaskata da mai zuwa bayansa, wato Yesu.” 5Da suka ji haka, aka yi musu baftisma da sunan Ubangiji Yesu. 6Da Bulus ya ɗora musu hannu, Ruhu Mai Tsarki ya sauko musu, suka kuwa yi magana da waɗansu harsuna, suna annabci. 7Su wajen goma sha biyu ne duka duka.
8Sai ya shiga majami'a yana wa'azi gabagaɗi, ya kuma yi wata uku yana muhawwara da su, yana kuma rinjayarsu a kan al'amarin Mulkin Allah. 9Amma da waɗansu suka taurare, suka ƙi ba da gaskiya, suna kushen wannan hanya a gaban jama'a, sai ya rabu da su, ya keɓe masu bi, yana ta muhawwara da su a kowace rana a makarantar Tiranas. 10Shekara biyu ana wannan, har dukan mazaunan ƙasar Asiya suka ji Maganar Ubangiji, Yahudawa da al'ummai duka.
11Ta hannun Bulus kuma Allah ya yi waɗansu mu'ujizai da ba a saba gani ba, 12har akan wa marasa lafiya adikansa, ko tufafinsa da yake sawa yana aiki, sun kuwa warke daga cuce-cucensu, baƙaƙen aljannu kuma sun rabu da su. 13Sai waɗansu Yahudawa masu yawo gari gari, matsubbata, suka yi ƙoƙarin kama sunan Ubangiji Yesu ga masu baƙaƙen aljannu, suna cewa, “Mun umarce ku da sunan Yesun nan da Bulus yake wa'azi.” 14To, akwai 'ya'ya bakwai maza, na wani babban firist na Yahudawa, mai suna Siba, duk suna yin wannan abu. 15Amma aljanin ya amsa musu ya ce, “Yesu dai na san shi, na kuma san Bulus, to, ku kuma su wane ne?” 16Mutumin nan mai aljanin sai ya daka tsalle, ya fāɗa musu, ya fi ƙarfinsu dukkansu, ya ci ɗunguminsu, har suka fita daga gidan a guje, a tuɓe, suna masu rauni. 17Wannan abu fa ya sanu ga dukan mazaunan Afisa, Yahudawa da al'ummai duka, duka kuma tsoro ya kama su, aka kuwa ɗaukaka sunan Ubangiji Yesu. 18Da yawa kuma daga cikin waɗanda suka ba da gaskiya suka zo, suna bayyana ayyukansu a fili. 19Mutane da yawa kuwa masu yin sihiri, suka tattaro littattafansu suka ƙone a gaban jama'a duka. Da suka yi wa littattafan nan kima, sai suka ga sun kai kuɗi azurfa dubu hamsin. 20Sai kuma Maganar Ubangiji ta ƙara haɓaka, ta kuma fifita ƙwarai.
21Bayan waɗannan al'amura Bulus ya ƙudura a ransa, cewa in ya zazzaga ƙasar Makidoniya da ta Akaya, za shi Urushalima, ya kuma ce, “Bayan da na je can, lalle ne kuma in je in ga birnin Roma.” 22Da ya aiki mataimakansa biyu Makidoniya, wato Timoti da Arastas, shi kuwa ya ɗan dakata a ƙasar Asiya.
23A lokacin nan kuwa ba ƙaramin hargitsi aka yi a game da wannan hanya ba. 24Domin akwai wani maƙerin farfaru, mai suna Dimitiriyas, mai ƙera surorin haikalin Artimas da azurfa, ba kuwa ƙaramar riba yake jawo wa masu yin wannan sana'a ba. 25Sai ya tara su da duk ma'aikatan irin wannan sana'a, ya ce, “Ya ku jama'a, kun sani fa da sana'ar nan muke arziki. 26Kuna kuwa ji, kuna gani, ba a nan Afisa kawai ba, kusan ma a duk ƙasar Asiya, Bulus ɗin nan ya rinjayi mutane masu yawan gaske, ya juyar da su, yana cewa, allolin da mutum ya ƙera ba alloli ba ne. 27Ga shi kuma, akwai hatsari, ba cewa cinikinmu kawai ne zai zama wulakantacce ba, har ma haikalin nan na uwargijiya Artimas mai girma zai zama ba a bakin kome ba, har kuma a raba ta da darajarta, ita da duk ƙasar Asiya, kai, har duniya ma duka suke bauta wa.”
28Da suka ji haka suka hasala ƙwarai, suka kuma ɗaga murya gaba ɗaya suna cewa, “Girma yā tabbata ga Artimas ta Afisawa!” 29Sai garin duk ya ruɗe, jama'a suka ruga zuwa dandali da nufi ɗaya, suna Gayus da Aristarkus, mutanen Makidoniya, abokan tafiyar Bulus. 30Bulus ya so shiga taron nan, amma masu bi suka hana shi. 31Waɗansu zaɓaɓɓun mutanen ƙasar Asiya, waɗanda suke abokansa, su ma suka aika masa, suka roƙe shi kada ya kuskura ya shiga dandalin nan. 32Taron kuwa, waɗansu suka ta da murya suka ce kaza, waɗansu suka ce kaza, don duk taron a ruɗe yake, yawancinsu ma ba su san dalilin da ya sa suka taru ba. 33Da Yahudawa suka gabatar da Iskandari, waɗansu suka ɗauka a kan shi ne sanadin abin. Iskandari kuwa ya ɗaga hannu a yi shiru, don ya kawo musu hanzari, 34amma da suka fahimci, cewa shi Bayahude ne, suka ɗaga murya gaba ɗaya har wajen sa'a biyu, suna ta cewa, “Girma yā tabbata ga Artimas ta Afisawa!”
35To, da marubucin garin ya kwantar da hankalin jama'a, ya ce, “Ku mutanen Afisa! Wane mutum ne bai san cewa musamman birnin Afisawa ne yake kula da haikalin mai girma Artimas ba, da kuma dutsen nan da ya faɗo daga sama? 36To, da yake ba dama a yi musun waɗannan abubuwa, ai, ya kamata ku natsu, kada ku yi kome da garaje. 37Ga shi, kun kawo mutanen nan, su kuwa ba su yi sata a ɗakin uwargijiya ba, ba su kuma saɓi uwargijiyarmu ba. 38To, in Dimitiriyas da abokan sana'arsa suna da wata magana a game da wani, ai, ga ɗakin shari'a a buɗe, ga kuma mahukunta, sai su kai ƙara. 39Amma in wani abu kuke nema dabam, to, ai, sai a daidaita a majalisa ke ke nan. 40Hakika muna a cikin hatsarin amsa ƙara a kan tawaye saboda al'amarin nan na yau, tun da yake ba za mu iya ba da wani hanzari a game da taron hargitsin nan ba.” 41Da ya faɗi haka ya sallami taron.
1Bayan hargowar nan ta kwanta, Bulus ya kira masu bi, bayar da ya ƙarfafa musu zuciya, ya yi bankwana da su, ya tafi ƙasar Makidoniya. 2Da ya zazzaga lardin nan, ya kuma ƙarfafa masu zuciya ƙwarai, ya zo ƙasar Hellas, 3ya yi wata uku a nan. Da Yahudawa suka ƙulla masa makirci, a sa'ad da zai tashi a jirgin ruwa zuwa ƙasar Suriya, ya yi niyyar komawa ta ƙasar Makidoniya. 4Subataras Babiriye, ɗan Burus, shi ya raka shi, tare da Aristarkus da Sakundas, mutanen Tasalonika, da Gayus Badarbe, da Timoti, har ma da Tikikus da Tarofimas, mutanen Asiya, 5waɗanda suka riga tafiya suka jira mu a Taruwasa. 6Mu kuwa muka tashi daga Filibi a jirgin ruwa, bayan idin abinci marar yisti, muka iske su a Taruwasa bayan kwana biyar. A nan muka zauna har kwana bakwai.
7A ranar farko ta mako kuma, da muka taru don gutsuttsura gurasa, Bulus ya yi masu jawabi, don ya yi niyyar rashi kashegari, sai ya yi ta jan jawabin nasa har tsakar dare. 8Akwai kuwa fitilu da yawa a benen da muka taru. 9Da wani saurayi a zaune a kan taga, mai suna Aftikos, sai barci ya ci ƙarfinsa sa'ad da Bulus yake ta tsawaita jawabi, da barci mai nauyi ya kwashe shi, sai ya faɗo daga can hawa na uku, aka ɗauke shi matacce. 10Amma Bulus ya sauka ƙasa, ya miƙe a kansa, ya rungume shi, ya ce, “Kada ku damu, ai, yana da rai.” 11Da Bulus ya koma sama, ya gutsuttsura gurasa ya ci, ya daɗe yana magana da su, har gari ya waye, sa'an nan ya tashi. 12Sai suka tafi da saurayin nan a raye, daɗin da suka ji kuwa ba kaɗan ba ne.
13Mu kuwa muka yi gaba zuwa jirgin, muka miƙa sai Asus da nufin ɗaukar Bulus daga can, don dā ma haka ya shirya, shi kuwa ya yi niyyar bi ta ƙasa. 14Da ya same mu a Asus, muka ɗauke shi a jirgin, muka zo Mitilini. 15Daga nan kuma muna tafe a jirgin ruwan dai, kashegari kuma sai ga mu daura da tsibirin Kiyos. Kashegari kuma, ga mu a tsibirin Samas, wani kashegari kuma sai Militas. 16Dā ma kuwa Bulus ya ƙudura zai wuce Afisa a cikin jirgin, don kada ya yi jinkiri a Asiya, domin yana sauri, ni mai yiwuwa ne ma, ya kai Urushalima a ranar Fentikos.
17Daga Militas ne ya aika Afisa a kira masa dattawan ikilisiya. 18Da suka zo wurinsa sai ya ce musu, “Ku da kanku kun san irin zaman da na yi a cikinku, tun ran da na sa ƙafata a ƙasar Asiya, 19ina bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali'u, har da hawaye, da gwaggwarmaya iri iri da na sha a game da makircin Yahudawa. 20Kun kuma san yadda ban ji nauyin sanar da ku kowane abu mai amfani ba, ina koya muku a sarari, da kuma gida gida, 21ina tabbatar wa Yahudawa da al'ummai duka sosai wajibcin tuba ga Allah, da kuma gaskatawa da Ubangijinmu Yesu. 22To, ga shi kuma, a yanzu zan tafi Urushalima, Ruhu yana iza ni, ban kuwa san abin da zai same ni a can ba, 23sai dai Ruhu Mai Tsarki yakan riƙa tabbatar mini a kowane gari, cewa ɗauri da shan wuya na dākona. 24Amma ni ban mai da raina a bakin kome ba, bai kuma dame ni ba, muddin zan iya cikasa tserena da kuma hidimar da na karɓa daga gun Ubangiji Yesu, in shaidar da bisharar alherin Allah. 25To, ga shi, a yanzu na san dukanku ba za ku ƙara ganina ba, ku da na zazzaga a cikinku ina yi muku bisharar Mulkin Allah. 26Saboda haka ina dai tabbatar muku a yau, cewa na kuɓuta daga hakkin kowa, 27domin kuwa ban ji nauyin sanar da ku dukan nufin Allah ba. 28Ku kula da kanku, da kuma duk garken da Ruhu Mai Tsarki ya sa ku ku zama masu kula da shi, kuna kiwon Ikilisiyar Allah wadda ya sama wa kansa da jininsa. 29Na sani bayan tashina waɗansu mugayen kyarketai za su shigo a cikinku, ba kuwa za su ji tausayin garken ba. 30Har ma a cikinku waɗansu mutane za su taso, suna maganganun da ba sa kan hanya, don su jawo masu bi a gare su. 31Saboda haka sai ku zauna a faɗake, ku tuna, shekara uku ke nan ba dare ba rana, ban fasa yi wa kowa gargaɗi ba, har da hawaye. 32To, a yanzu na danƙa ku ga Ubangiji, maganar alherinsa kuma tă kiyaye ku, wadda ita take da ikon inganta ku, ta kuma ba ku gādo tare da dukan tsarkaka. 33Ban yi ƙyashin kuɗin kowa ba, ko kuwa tufafin wani. 34Ku da kanku kun sani hannuwan nan nawa su suka biya mini bukace-bukacena, da na waɗanda suke tare da ni. 35Na zamar muku abin misali ta kowace hanya, cewa ta wahalar aiki haka lalle ne a taimaki masu ƙaramin ƙarfi, kuna kuma tunawa da Maganar Ubangiji Yesu da ya ce, “‘Bayarwa ta fi karɓa albarka.”
36Da Bulus ya faɗi haka, ya durƙusa, duka suka yi addu'a tare. 37Sai duk suka fashe da kuka, suka rungume Bulus, suna ta sumbantarsa, 38suna baƙin ciki tun ba ma saboda maganar da ya faɗa ba, cewa ba za su ƙara ganinsa ba. Daga nan suka rako shi har bakin jirgi.
1Sa'ad da muka rabu da su da ƙyar, muka shiga jirgi muka miƙa sosai zuwa tsibirin Kos, kashegari kuma sai Rodusa, daga nan kuma sai Batara. 2Da muka sami jirgi mai hayewa zuwa ƙasar Finikiya, muka shiga muka tafi. 3Da muka tsinkayo tsibirin Kubrus, muka mai da shi hagun, muka ci gaba zuwa ƙasar Suriya, muka sauka a Taya, don a nan ne jirgin zai sauke kayansa. 4Da muka sami inda masu bi suke, muka zauna a nan kwana bakwai. Sai Ruhu ya iza su suka gaya wa Bulus kada ya je Urushalima. 5Amma da lokacin tashinmu ya yi, muka tashi muka ci gaba da tafiyarmu, dukansu kuma har da matansu da 'ya'yansu, suka raka mu har bayan gari, sa'an nan muka durƙusa a kan gaci, muka yi addu'a, muka yi bankwana da juna. 6Sai muka shiga jirgi, su kuma suka koma gida.
7Da muka gama tafiyarmu daga Taya, muka isa Talamayas, sai muka gaisa da 'yan'uwa, muka kuma kwana ɗaya a wurinsu. 8Kashegari muka tashi muka zo Kaisariya, muka shiga gidan Filibus mai yin bishara, wanda yake ɗaya daga cikin bakwai ɗin nan, muka sauka a wurinsa. 9Shi kuwa yana da 'ya'ya huɗu 'yan mata, masu yin annabci. 10To, muna nan a zaune 'yan kwanaki, sai wani annabi, mai suna Agabas, ya zo daga Yahudiya. 11Da ya zo gare mu, ya ɗauki ɗamarar Bulus ya ɗaure kansa sawu da hannu, ya ce, “Ga abin da Ruhu Mai Tsarki ya ce, “‘Haka Yahudawan Urushalima za su ɗaure mai wannan ɗamara, su kuma bashe shi ga al'ummai.” 12Da muka ji haka, mu da waɗanda suke a wurin muka roƙi Bulus kada ya je Urushalima. 13Sai Bulus ya amsa ya ce, “Me ke nan kuke yi, kuna kuka kuna baƙanta mini rai? Ai, ni a shirye nake, ba ma a ɗaure ni kawai ba, har ma a kashe ni a Urushalima saboda sunan Ubangiji Yesu.” 14Da dai ya ƙi rarrasuwa, muka yi shiru, muka ce, “Ubangiji ya yi yadda ya so.”
15Bayan 'yan kwanakin nan muka shirya muka tafi Urushalima. 16Waɗansu masu bi daga Kaisariya suka rako mu, suka kawo mu wurin Manason, mutumin Kubrus, wani daɗaɗɗen mai bi, wanda za mu sauka a gunsa.
17Da muka zo Urushalima, 'yan'uwa suka karɓe mu da murna. 18Kashegari Bulus ya tafi tare da mu a wurin Yakubu, dattawan ikilisiya kuwa duk suna nan. 19Bayan da ya gaisa da su, sai ya shiga bayyana musu filla abubuwan da Allah ya yi a cikin al'ummai ta wurin hidimarsa. 20Su kuwa da suka ji haka, suka ɗaukaka Allah. Suka ce wa Bulus, “To, kā gani ɗan'uwa, dubban mutane sun ba da gaskiya a cikin Yahudawa, dukansu kuwa masu himma ne a wajen bin Shari'a. 21An kuwa sha gaya musu labarinka, cewa kai ne kake koya wa dukan Yahudawan da suke a cikin al'ummai su yar da Shari'ar Musa. Kuma kana ce musu kada su yi wa 'ya'yansu kaciya, ko kuwa su bi al'adu. 22To, ƙaƙa ke nan? Lalle za su ji labarin zuwanka. 23Saboda haka sai ka yi abin da za mu faɗa maka. Muna da mutum huɗu da suka ɗauki wa'adi. 24Sai ka tafi da su ku tsarkaka gaba ɗaya, ka kuma biya musu kome don su samu su yi aski. Ta haka, kowa zai sani duk abin da aka gaya musu a game da kai, ba wata gaskiya a ciki, kai kuma kana kiyaye Shari'a. 25Amma a game da al'ummai da suka ba da gaskiya, mun aika da wasiƙa a kan mun hukunta, cewa su guji cin abin da aka yanka wa gunki, da fasikanci, da cin abin da aka maƙure, da kuma cin nama tare da jini.” 26Sa'an nan Bulus ya ɗibi mutanen nan, kashegari kuma da suka tsarkaka tare, sai ya shiga Haikali domin ya sanar da ranar cikar tsarkakewar tasu, wato ranar da za a ba da sadaka saboda kowannensu.
27Da kwana bakwai ɗin suka yi kusan cika, Yahudawan ƙasar Asiya suka gan shi a Haikalin, sai suka zuga taron duka, suka danƙe shi, 28suna ta ihu suna cewa, “Ya ku 'yan'uwa Isra'ilawa, ku taimaka! Ga mutumin da yake bi ko'ina yana koya wa mutane su raina jama'armu da Shari'a, da kuma wannan wuri. Banda haka kuma har ma ya kawo al'ummai a cikin Haikalin, ya ƙazantar da wurin nan tsattsarka.” 29Don dā ma can sun ga Tarofimas Ba'afise tare da shi a cikin gari, sun kuma zaci Bulus ya kawo shi a cikin Haikalin. 30Sai duk garin ya ruɗe, jama'a suka ɗungumo a guje suka danƙe Bulus, suka ja shi a waje daga Haikalin, nan da nan kuma aka rufe ƙofofi. 31Suna neman kashe shi ke nan, sai labari ya kai ga shugaban ƙungiyar yaƙi, Urushalima duk ta hargitse. 32A nan tāke ya ɗibi soja da jarumawa, suka ruga zuwa wajensu. Su kuwa da ganin shugaban da soja suka daina dūkan Bulus. 33Sai shugaban ya matsa kusa ya kama Bulus, ya yi umarni a ɗaure shi da sarƙa biyu, sa'an nan ya tambaya ko shi wane ne, da abin da kuma ya yi. 34Taron kuwa suka ɗau kururuwa, waɗansu suka ce kaza, waɗansu suka ce kaza. Don tsananin hargowa ma har ya kasa samun ainihin tushen maganar, ya yi umarni a kai shi kagarar sojoji. 35Da Bulus ya zo ga bakin matakala, sai da soja suka kinkime shi saboda haukan taron, 36don taron jama'a suna dannowa a bayansu, suna ihu suna cewa, “A yi da shi!”
37An yi kusan shigar da Bulus a kagarar sojoji ke nan, sai ya ce wa shugaban, “Ko ka yarda in yi magana da kai?” Sai shugaban ya ce, “Ashe, ka iya Helenanci? 38Shin, ba kai ne Bamasaren nan da shekarun baya ya haddasa tawaye ba, har ya ja mutanen nan dubu huɗu masu kisankai zuwa jeji?” 39Sai Bulus ya amsa ya ce, “Ai, ni Bayahude ne na Tarsus ta ƙasar Kilikiya, ɗan shahararren birni, ina roƙonka ka bar ni in yi wa mutane jawabi.” 40Da ya ba shi izini, sai Bulus ya tsaya a kan matakala, ya ɗaga wa jama'a hannu su yi shiru. Da suka yi tsit, sai ya yi musu magana da Yahudanci.
1“Ya ku 'yan'uwa da shugabanni, ku ji hanzarin da zan kawo muku a yanzu.”
2Da suka ji ya yi musu magana da Yahudanci, sai suka ƙara natsuwa. Sa'an nan ya ce, 3“Ni bayahude ne, haifaffen Tarsus, ta ƙasar Kilikiya, amma a nan garin na yi girma, aka kuma karantar da ni a wurin Gamaliyal, bisa ga tsarin tsanantacciyar hanyar nan ta Shari'ar kakanninmu. Ina mai himmar bauta wa Allah, kamar yadda kuke a yau, 4har na tsananta wa masu bin wannan hanya, ina karkashe su, ina ɗaure mutane maza da mata, ina jefa su a kurkuku. 5Babban firist ma da dukan majalisar shugabannin jama'a za su iya shaidata, daga gunsu ne kuma na karɓi wasiƙu zuwa ga 'yan'uwanmu Yahudawa, na tafi Dimashƙu, don in ɗebo waɗanda suke can ma, in zo da su Urushalima a ɗaure, a azabta su.”
(A. M. 9.1-19; 26.12-18)
6“Ina a cikin tafiya, da na yi kusa da Dimashƙu, a wajen rana tsaka, kwamfa sai wani matsanancin haske ya bayyano daga sama, ya haskaka kewaye da ni. 7Sai na fāɗi, na kuma ji wata murya tana ce mini, “‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?” 8Ni kuma na amsa na ce, “‘Wane ne kai, ya Ubangiji?” Sai ya ce mini, “‘Ni ne Yesu Banazare wanda kake tsananta wa.” 9To, waɗanda suke tare da ni suka ga hasken, amma ba su ji kalmomin mai yi mini maganar nan ba. 10Sai na ce, “‘To, me zan yi, ya Ubangiji?” Sai ubangiji ya ce mini, “‘Tashi, ka shiga Dimashƙu, a can ne za a faɗa maka duk abin da aka ɗora maka ka yi.” 11Da na kāsa gani saboda tsananin hasken nan, sai waɗanda suke tare da ni suka yi mini jagora, har na isa Dimashƙu.
12“Sai kuma wani mai suna Hananiya, mai bautar Allah ne a wajen bin Shari'a, wanda duk Yahudawan da suke zaune a can suke yabo, 13ya zo ya tsaya a kusa da ni, ya ce mini, “‘Ya ɗan'uwana Shawulu, ganinka yă komo maka.” A nan tāke, sai ganina ya komo, na kuwa gan shi. 14Sai ya ce, “‘Allahn kakanninmu ya zaɓe ka don kă san nufinsa, ka ga Mai Adalcin nan, ka kuma ji jawabi daga bakinsa. 15Don za ka zama mashaidinsa ga dukan mutane a game da abin da ka gani, ka kuma ji. 16To, a yanzu me kake jira? Tashi, a yi maka baftisma a wanke zunubanka ta wurin kira bisa sunansa.”
17“Da na komo Urushalima, ina addu'a a Haikali, sai wahayi ya zo mini. 18Na gan shi, yana ce mini, “‘Yi sauri maza ka fita daga Urushalima, don ba za su yarda da shaidarka a kaina ba.” 19Ni kuma na ce, “‘Ya Ubangiji, ai, su ma kansu sun sani a kowace majami'a nakan ɗaɗɗaure waɗanda suka gaskata da kai, nakan kuma daddoke su. 20Sa'ad da kuma aka zub da jinin Istifanas, mashaidin nan naka, ni ma ina a tsaye a gun, ina goyon bayan abin da aka yi, har ma ina tsaron tufafin masu kisansa.” 21Sai ya ce mini, “‘Tashi ka tafi, zan aike ka can nesa a wurin al'ummai.”
22Suna ta sauraronsa har ya iso kalmar nan, sai suka ɗau ihu suka ce, “A kashe shi! A raba irin mutumin nan da duniya, bai kyautu ya rayu ba!” 23Da suka dinga ihu suna kaɗa mayafansu suna ta ature da ƙura, 24sai shugaba ya yi umarni a kai Bulus kagarar soja a tuhume shi da bulala, don yă san abin da ya sa suke masa ihu haka. 25Bayan da suka ɗaɗɗaure shi da tsirkiya, Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye kusa, “Ashe, ya halatta a gare ka ka yi wa mutumin da yake da 'yancin Roma bulala, ba ko bin ba'asi?” 26Da jarumin ya ji haka, sai ya je ya shaida wa shugaban, ya ce, “Me kake shirin yi ne? Mutumin nan fa Barome ne.” 27Sai shugaban ya zo ya ce wa Bulus, “Faɗa mini gaskiya, kai kuwa Barome ne?” Sai ya ce, “I.” 28Sai shugaban ya amsa ya ce, “Ni fa da kuɗi masu yawa na sami 'yancin nan.” Bulus ya ce, “Ka ga ni kuwa da shi aka haife ni.” 29Saboda haka, waɗanda suke shirin tuhumarsa, suka rabu da shi nan da nan. Shi ma shugaban da ya fahimci cewa, Bulus Barome ne, sai ya tsorata, ga shi kuwa, ya ɗaure shi.
30Kashegari kuma da shugaban ya so sanin ainihin ƙarar da Yahudawa suke yi a kan Bulus, sai ya kwance shi, ya yi umarni domin manyan firistoci da dukan majalisa su taru, sa'an nan ya sauko da Bulus ya tsai da shi a gabansu.
1Sai Bulus ya zuba wa majalisar ido ya ce, “Ya ku 'yan'uwa, ku sani, bautar Allah nake yi da lamiri mai kyau har ya zuwa yau.” 2Sai Hananiya babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa. 3Sai Bulus ya ce masa, “Kai munafiƙi, kai ma Allah zai buge ka! Ashe, wato kana zaune kana hukunta ni bisa ga Shari'a ne, ga shi kuwa kana yin umarni a doke ni, a saɓanin Shari'a?” 4Sai waɗanda ke tsaye a wurin suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?” 5Sai Bulus ya ce, “Ai, ban sani shi ne babban firist ba, 'yan'uwa, don a rubuce yake cewa, “‘Kada ka munana shugaban jama'a.”
6Amma da Bulus ya ga sashe ɗaya Sadukiyawa ne, ɗayan kuma Farisiyawa, ya ɗaga murya a majalisar ya ce, “Ya 'yan'uwa, ni ma Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ga shi kuwa, saboda na sa zuciya ga tashin matattu ne ake yi mini shari'a.” 7Da ya faɗi haka sai gardama ta tashi a tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, har taron ya rabu biyu. 8Sadukiyawa sun ce, suna cewa ba tashin matattu, ba kuma mala'iku, ko ruhu. Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai. 9Sai ƙasaitacciyar hargowa ta tashi, waɗansu malamai kuma na cikin ɗariƙar Farisiyawa suka miƙe a tsaye, suka yi ta yin matsananciyar jayayya, suna cewa, “Mu ba mu ga laifin mutumin nan ba. In wani ruhu ne ko mala'ika ya yi masa magana fa?” 10Da gardamar ta yi tsanani, don gudun kada su yi kaca-kaca da Bulus, shugaban ya umarci sojan su sauka su ƙwato shi daga wurinsu ƙarfi da yaji, su kawo shi a kagarar soja.
11Da daddare sai Ubangiji ya tsaya a kusa da Bulus, ya ce, “Ka yi ƙarfin hali, don kamar yadda ka shaide ni a Urushalima, haka kuma lalle ne ka shaide ni a Roma.”
12Da gari ya waye, Yahudawa suka gama baki suka yi rantsuwa, cewa ba za su ci ba, ba za su sha ba, sai sun kashe Bulus. 13Waɗanda suka ƙulla wannan makirci kuwa sun fi mutum arba'in. 14Sai suka je wurin manyan firistoci da shugabanni, suka ce, “Mun yi wata babbar rantsuwa, cewa za mu zauna ba ci ba sha sai mun kashe Bulus. 15Saboda haka, a yanzu ku da majalisa ku shaida wa shugaban soja ya kawo muku shi, kamar kuna so ne ku ƙara bincika maganarsa sosai, mu kuwa a shirye muke mu kashe shi kafin ya iso.”
16To, ɗan 'yar'uwar Bulus ya ji labarin farkon da za su yi, ya kuma je ya shiga kagarar soja ya gaya wa Bulus. 17Bulus kuwa ya kira wani jarumi ya ce, “Ka kai saurayin nan wurin shugaba, yana da wata magana da zai faɗa masa.” 18Sai jarumin ya ɗauki saurayin ya kai shi gun shugaba, ya ce, “Ɗan sarƙan nan, Bulus, ya kira ni, ya roƙe ni in kawo saurayin nan a wurinka, don yana da wata maganar da zai gaya maka.” 19Sai shugaban ya kama hannun saurayin, ya ja shi a waje ɗaya, ya tambaye shi a keɓance, “Wace magana za ka gaya mini?” 20Yaron ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kai musu Bulus majalisa gobe, kamar suna so su ƙara bincika maganarsa sosai. 21Amma kada ka yardar musu, don fiye da mutum arba'in daga cikinsu suna fakonsa, sun kuma yi rantsuwa a kan ba za su ci ba, ba za su sha ba, sai sun kashe shi. A yanzu kuwa a shirye suke, yardarka kawai suka jira.” 22Sai shugaban ya sallami saurayin ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka sanar da ni maganar nan.”
23Sa'an nan ya kira jarumi biyu ya ce, “Ku shirya soja metan, da barade saba'in, da 'yan māsu metan, su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.” 24Ya kuma yi umarni su shirya wa Bulus dabbobin da zai hau, don su kai shi wurin mai mulki Filikus lafiya. 25Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka:
26“Daga Kalaudiyas Lisiyas zuwa ga mafifici mai mulki Filikus. Gaisuwa mai yawa. 27Bayan haka mutumin nan, Yahudawa sun kama shi, suna kuma gab da kashe shi, sai na yi farat na je da soja na ƙwato shi, saboda na ji cewa shi Barome ne. 28Da nake so in jin laifin da suke zarginsa a kai, sai na kai shi majalisarsu. 29Na kuwa tarar suna zarginsa a kan maganar Shari'arsu, amma laifin da suka ɗora masa bai kisa ko ɗauri ba. 30Da aka buɗa mini cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, nan da nan na aika da shi a gare ka, na kuma umarci masu ƙararsa su faɗi ƙararsu a gabanka. Wassalam.”
31Saboda haka, sojan suka ɗauki Bulus, kamar yadda aka umarce su, suka kai shi Antibatiris da daddare. 32Kashegari kuma suka bar barade su ci gaba da shi, su kuwa suka koma kagarar soja. 33Da baraden suka isa Kaisariya, suka ba mai mulkin wasiƙar, suka kai Bulus a gabansa. 34Da ya karanta wasiƙar, ya tambayi Bulus ko shi mutumin wane lardi ne? Da ya ji daga Kilikiya yake, 35sai ya ce, “Zan saurari maganarka duka, in masu ƙararka sun zo.” Sai kuma ya yi umarni a tsare shi a fadar Hirudus.
1Bayan kwana biyar sai babban firist, Hananiya, ya zo tare da waɗansu shugabanni, da kuma wani lauya, mai suna Tartulus, suka yi ƙarar Bulus a gaban mai mulki.
2Da aka kirawo Tartulus, ya shiga kai ƙarar Bulus, ya ce, “Ya mafifici Filikus, tun da yake ta gare ka ne muke zaman lafiya ƙwarai, ta tsinkayarka ne kuma ake kyautata zaman jama'armu, 3kullum muna yarda da haka ƙwarai a ko'ina, tare da godiya ba iyaka. 4Amma don kada in gajiyad da kai, ina roƙonka a cikin nasiharka, ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu. 5Mun tarar da mutumin nan fitinanne ne, yana ta da hargitsi a tsakanin Yahudawa ko'ina a duniya, shi kuma ne turun ɗariƙar Nazarawa. 6Har ma yana nema ya tozarta Haikali, amma muka kama shi.[Niyyarmu ce mu hukunta shi bisa ga shari'armu. 7Amma shugaba Lisiyas ya zo ya ƙwace shi daga hannunmu ƙarfi da yaji, 8ya yi umarni masu ƙararsa su zo a gabanka.] In kuwa ka tuhume shi da kanka, za ka iya tabbatarwa daga bakinsa duk ƙarar da muke tāsarwa.”
9Yahudawa ma suka goyi bayan haka, suna tabbatarwa haka abin yake.
10Da mai mulki ya alamta wa Bulus ya yi magana, sai ya amsa ya ce, “Tun da na sani ka yi shekaru da yawa kana yi wa jama'ar nan shari'a, da farin ciki zan kawo hanzarina. 11Ai, ka iya tabbatarwa, bai fi kwana goma sha biyu ba tun da na tafi Urushalima yin sujada. 12Ba su kuwa taɓa samuna ina muhawwara da kowa ba, ko kuwa ta da husuma har mutane su taru a Haikali, ko a majami'u, ko kuwa a cikin birni ba. 13Ba kuma za su iya tabbatar maka abin da yanzu suke ƙarata a kai ba. 14Amma na yarda da cewa, bisa ga hanyar nan da suke kira “‘Ɗariƙa” nake bauta wa Allahn kakanninmu, nake kuma gaskata duk abin da yake a rubuce a cikin Attaura da kuma littattafan annabawa. 15Ina sa zuciya ga Allah, yadda su waɗannan ma suke sawa, wato za a ta da matattu, masu adalci da marasa adalci duka. 16Saboda haka, a kullum nake himma in kasance da lamiri marar abin zargi a wurin Allah da wurin mutane. 17To, bayan 'yan shekaru sai na je domin in kai gudunmawa ga jama'armu, in kuma yi sadaka. 18Ina cikin yin haka sai suka same ni a tsarkake a Haikali, ba kuwa da wani taro ba, balle hargowa. Amma akwai waɗansu Yahudawa daga ƙasar Asiyaū 19su ne kuwa ya kamata su zo nan a gabanka su yi ƙarata, in suna da wata magana a game da ni. 20Ko kuwa waɗannan mutane da kansu su faɗi laifina da suka samu, sa'ad da na tsaya a gaban majalisa, 21sai ko maganar nan ɗaya tak, da na ɗaga murya na faɗa, sa'ad da nake a tsaye a cikinsu, cewa, “‘A game da maganar tashin matattu ake yi mini shari'a a gabanku yau.”
22Filikus kuwa da yake yana da sahihin ilimi a game da wannan hanya ya dakatar da su, ya ce, “In shugaba Lisiyas ya iso, zan yanke muku shari'a.” 23Ya kuma ba jarumi umarni ya tsare Bulus, amma ya sassauta masa, kada kuwa ya hana mutanensa zuwa wurinsa su kula da shi.
24Bayan 'yan kwanaki Filikus ya zo tare da matarsa, Durusila, wata Bayahudiya. Sai ya aika a zo da Bulus, ya kuwa saurare shi a kan maganar gaskatawa da Almasihu Yesu. 25Bulus yana ba da bayani a kan adalci, da kamunkai, da kuma hukuncin nan mai zuwa, Filikus ya kaɗu, ya kāda baki ya ce, “Yanzu kam, sai ka koma. In na sami zarafi nā kira ka.” 26Don yana sa rai Bulus zai ba shi kuɗi, shi ya sa ya yi ta kiransa a kai a kai, yana zance da shi. 27Amma bayan shekara biyu sai Borkiyas Festas ya gāji Filikus. Filikus kuwa don neman farin jini a wurin Yahudawa, ya bar Bulus a ɗaure.
1To, da Festas ya iso lardinsa, bayan kwana uku sai ya tashi daga Kaisariya ya tafi Urushalima. 2Sai manyan firistoci da manyan Yahudawa suka kai ƙarar Bulus a gunsa, suka roƙe shi 3ya kyauta musu, ya aika a zo da shi Urushalima, alhali kuwa sun shirya 'yan kwanto su kashe shi a hanya. 4Amma Festas ya amsa ya ce, “Bulus yana a tsare a Kaisariya, ni ma kuwa da kaina ina niyyar zuwa a can a kwanan nan.” 5Ya kuma ce, “Saboda haka, sai waɗansu manya a cikinku su taho tare da ni, in kuwa mutumin nan yana da wani laifi, su yi ƙararsa.”
6Bai fi kwana takwas ko gama a wurinsu ba, sai ya tafi Kaisariya. Kashegari kuma ya zauna a kan gadon shari'a, ya yi umarni a zo da Bulus. 7Da ya zo, Yahudawan da suka zo daga Urushalima suka kewaye shi a tsaitsaye, suna ta kawo ƙararraki masu yawa masu tsanani a game da shi, waɗanda ma suka kasa tabbatarwa. 8Amma Bulus ya kawo hanzarinsa ya ce, “Ni ban yi wani laifi a game da shari'ar Yahudawa, ko Haikali, ko a game da Kaisar ba, ko kaɗan.” 9Festas kuwa don neman farin jini a wurin Yahudawa, ya amsa ya ce wa Bulus, “Ka yarda ka je Urushalima a yi maka shari'a a can a kan waɗannan abubuwa a gabana?” 10Amma Bulus ya ce, “Ai, a tsaye nake a majalisar Kaisar, a inda ya kamata a yi mini shari'a. Ban yi wa Yahudawa wani laifi ba, kai kanka kuwa ka san da haka sarai. 11To, in ni mai laifi ne, har na aikata abin da ya isa kisa, ai, ba zan guji a kashe ni ba, amma in ba wata gaskiya a cikin ƙarata da suke yi, to, ba mai iya bashe ni a gare su don a faranta musu rai. Na nema a ɗaukaka ƙarata a gaban Kaisar.” 12Bayan da Festas ya yi shawara da majalisa, sai ya amsa ya ce, “To, ka nema a ɗaukaka ƙararka a gaban Kaisar! A gun Kaisar kuwa za ka tafi.”
13Bayan 'yan kwanaki sai sarki Agaribas da Barniki, suka zo Kaisariya don su yi wa Festas maraba. 14Da yake kuma sun yi kwanaki da dama a can, sai Festas ya rattaba wa sarki labarin Bulus, ya ce, “Akwai wani mutumin da Filikus ya bari a ɗaure, 15wanda sa'ad da nake Urushalima manyan firistoci da shugabannin Yahudawa suka kawo mini ƙararsa, suka roƙe ni in yi masa hukunci. 16Ni kuwa na amsa musu na ce, ba al'adar Romawa a yi wa wani hukunci, don a faranta wa wani rai, ba tare da masu ƙarar, da wanda aka kai ƙara, sun gurfana a gaban shari'a ba, ya kuma sami damar kawo hanzarinsa game da ƙarar da aka tāsar. 17Saboda haka, da suka zo nan tare, ban yi wani jinkiri ba, sai kawai na hau akan gadon shari'a kashegari, na kuma yi umarni a kawo mutumin. 18Da masu ƙarar suka tashi a tsaye, ba su kawo wata mummunar ƙara yadda na zata a game da shi ba, 19sai dai waɗansu maganganu da suka ɗora masa a game da addininsu, da kuma wani, shi Yesu, wanda ya mutu, amma Bulus ya tsaya a kan, cewa lallai yana da rai. 20Ni kuwa da na rasa yadda zan bincika waɗannan abubuwa, sai na tambayi Bulus ko ya yarda ya je Urushalima a yi masa shari'a a can a kan waɗannan abubuwa. 21Amma da Bulus ya nema a dakatar da maganarsa sai Augustas ya duba ta, sai na yi umarni a tsare shi har kafin in aika da shi zuwa a gun Kaisar.” 22Sai Agaribas ya ce wa Festas, “Ni ma dai na so in saurari mutumin nan da kaina.” Festas ya ce, “Kā kuwa ji shi gobe.”
23To kashegari sai Agaribas da Barniki suka zo a cikin alfarma, suka shiga ɗakin majalisa tare da shugabannin yaƙi da kuma jigajigan garin. Sai aka shigo da Bulus sai da umarnin Festas. 24Sai Festas ya ce, “Ya sarki Agaribas, da dukan mutanen da suke a tare da mu, kun ga mutumin nan da duk jama'ar Yahudawa suka kawo mini ƙararsa a Urushalima, da kuma nan, suna ihu, cewa bai kamata a bar shi da rai ba. 25Amma ni ban ga abin da ya yi wanda ya isa kisa ba. Tun da kuma shi kansa ya nema a mai da shari'arsa a gaban Augustas, na ƙudura in aika da shi zuwa wurinsa. 26Amma ba ni da wata tabbatacciyar magana da zan rubuta wa ubangidana a game da shi. Saboda haka na kawo shi a gabanku, musamman kuwa a gabanka, ya sarki Agaribas, don bayan an yi bincike, ko na abin da zan rubuta. 27Don ni, a ganina, wauta ce a aika da ɗan sarƙa, ba tare da an nuna laifofin da ya yi ba.”
1Daga nan, sai Agaribas ya ce wa Bulus, “An ba ka izinin yin magana.” Sa'an nan fa Bulus ya ɗaga hannu, ya fara kawo hanzarinsa ya ce, 2“Lalle na yi arziki, ya sarki Agaribas, da yake a gabanka ne zan kawo hanzarina yau a game da duk ƙarata da Yahudawa suka yi, 3musamman da yake gwani ne kai ga sanin al'adun Yahudawa da maganganunsu. Saboda haka, ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.
4“Irin zaman da na yi tun daga ƙuruciyata, wato tun da farko, a cikin jama'armu da kuma a Urushalima har ya zuwa yau, sananne ne ga dukan Yahudawa. 5Sun sani tun ainihi, in dai za su yarda su yi shaida, cewa lalle ni Bafarisiye ne bisa ga ɗariƙar nan da ta fi tsanani a cikin addinin nan namu. 6Ai, saboda na sa zuciya ga cikar alkawarin nan ne da Allah ya yi wa kakanninmu nake nan a tsaye a yi mini shari'a. 7Alkwarin nan kuwa, shi ne wanda kabilanmu goma sha biyu suke himmantuwa ga bauta wa Allah dare da rana, suna sa zuciya su ga cikarsa. Saboda sa zuciyar nan kuma fa Yahudawa suke ƙarata, ya sarki! 8Yaya cewa Allah yana ta da matattu sa'an nan, ya ƙi gaskatuwa a gare ku>
9“To, ni kaina ma a dā na ga kamar wajibi ne in yi abubuwa da yawa, na gāba da sunan Yesu Banazare. 10Na kuwa yi haka a Urushalima, har na sami izinin daga manyan firstoci, na kulle tsarkaka da yawa a kurkuku. Har ma a lokacin da ake kashe su ina goyon bayan yin haka ɗin. 11Na kuma sha gwada musu azaba a dukan majami'u, ina ƙoƙarin sa su yin saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.”
(A. M. 9.1-19; 22.6-16)
12“A cikin hali haka ne, ina tafiya Dimashƙu da izinin manyan firistoci da kuma saƙonsu, 13da rana a tsaka a hanya, ya sarki, na ga wani haske ya bayyana daga sama, fiye da hasken rana, duk ya haskaka kewaye da ni da abokan tafiyata. 14Da duk muka fāɗi, sai na ji wata murya tana ce mini da yahudanci, “‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Da wuya a gare ka ka yi ta shuri bisa a kan tsini.” 15Ni kuwa sai na ce, “‘Wane ne kai, ya Ubangiji?” Sai Ubangiji ya ce, “‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa. 16Amma tashi ka miƙe a tsaye, gama na bayyana a gare ka ne da wannan maƙasudi, wato in sa ka mai hidima, mashaidi kuma na abubuwan da ka gani a game da ni, da kuma abubuwa waɗanda zan bayyana maka a nan gaba. 17Zan tsirar da kai daga jama'ar nan da kuma al'ummai, waɗanda zan aike ka a gare su, 18domin ka buɗe musu ido, su juyo daga duhu zuwa haske, daga kuma mulkin Shaiɗan zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai, da kuma gādo tare da dukan tsarkaka saboda sun gaskata da ni.”
19“Saboda haka, ya sarki Agaribas, ban ƙi biyayya ga wahayin nan da ya zo mini daga Sama ba. 20Da fari, na yi wa mutanen Dimashƙu wa'azi, sa'an nan na yi a Urushalima da dukan kewayen ƙasar Yahudiya, sa'an nan kuma na yi wa al'ummai, cewa su tuba su juyo ga Allah, su kuma yi aikin da zai nuna tubarsu. 21Saboda wannan dalili ne Yahudawa suka kama ni a Haikali, har suna neman kashe ni. 22Da na sami taimakon Allah kuwa, ga ni a nan har yanzu, ina shaida wa babba da yaro, ba na faɗar kome sai abin da annabawa da Musa suka ce zai auku, 23cewa dai lalle ne Almasihu yă sha wuya, shi ne kuma zai fara tashi daga matattu, ya sanar da jama'ar nan da al'ummai haske.”
24Bulus yana cikin kawo hanzarinsa, sai Festas ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Bulus, kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.” 25Amma Bulus ya ce, “Ya mafifici Festas, ai, ban ruɗe ba, gaskiya nake faɗa, a cikin natsuwa kuwa. 26Ai, al'amarin nan sananne ne ga sarki, ina kuma masa magana gabagaɗi ne, gama na tabbata ba abin da ya kuɓuce wa hankalinsa a cikin al'amarin nan, don wannan abu ba a ɓoye aka yi shi ba. 27Ya sarki Agaribas, ka gaskata annabawa? Na dai sani ka gaskata.” 28Sai Agaribas ya ce wa Bulus, “Wato a ɗan wannan taƙaitaccen lokaci kake nufin mai da ni Kirista?” 29Bulus kuwa ya ce, “Ko a ɗan wannan, ko a mai yawa, ina fata ga Allah, ba kai kaɗai ba, har ma duk waɗanda suke saurarona a yau, su zama kamar yadda nake, sai dai banda sarƙar nan.”
30Sai sarki ya tashi, haka kuma mai mulki da Barniki, da waɗanda suke a zaune tare da su. 31Bayan sun keɓe a waje ɗaya, suka yi shawara, suka ce, “Ai, mutumin nan bai yi wani abin da ya isa kisa ko ɗauri ba.” 32Agaribas kuma ya ce wa Festas, “Ba don dai mutumin nan ya riga ya nemi ɗaukaka ƙararsa a gaban Kaisar ba, da sai a sake shi.”
1Da aka shirya mu tashi a jirgin ruwa zuwa ƙasar Italiya, sai suka danƙa Bulus da waɗansu 'yan sarƙa a hannun wani jarumi, mai suna Yuliyas, na ƙungiyar Augustas. 2Da muka shiga wani jirgi na Adaramitiya, mai shirin tashi zuwa waɗansu garuruwan da suke gaɓar Asiya, muka fara tafiya. Aristarkus kuwa, wani mutumin Tasalonika ta ƙasar Makidoniya, yana tare da mu. 3Kashegari ga mu a Sidon. Yuliyas kuwa ya yi wa Bulus alheri, ya ba shi izini ya je ya gano abokansa, su yi masa taimako. 4Da muka tashi daga nan a jirgin ruwa sai muka zaga ta bayan tsibirin Kubrus, saboda iska tana gāba da mu. 5Bayan da muka haye bahar ɗin da yake kusa da kasar Kilikiya da ta Bamfiliya, muka isa Mira ta ƙasar Likiya. 6A nan jarumin ya sami wani jirgin Iskandariya mai zuwa ƙasar Italiya, ya sa mu a ciki. 7Muka yi kwana da kwanaki muna tafiya kaɗan kaɗan, har da ƙyar muka kai kusa da Kinidas. Da dai iska ta hana mu ci gaba, muka zaga ta bayan tsibirin Karita kusa da Salmoni. 8Muna bin gefen gaɓarsa da ƙyar, har muka isa wani wuri mai suna Amintacciyar Mafaka, wadda take a kusa da birnin Lasiya.
9Da yake an ɓata lokaci mai yawa, tafiyar ma ta riga ta zama mai hatsari, lokacin azumi kuwa ya wuce, sai Bulus ya gargaɗe su, 10ya ce musu, “Ya ku jama'a, na dai ga tafiyar nan za ta zamanto da masifa da hasara mai yawa, ba ta kaya da jirgi kawai ba, har ma ta rayukanmu.” 11Amma jarumin soja, ya fi mai da hankali ga maganar mai tuƙin jirgin da kuma ta mai jirgin, a kan abin da Bulus ya faɗa. 12Da yake mafakar nan ba ta kamaci jirage su ci damuna a ciki ba, sai yawanci suka kawo shawara a tashi daga nan, ko ta ƙaƙa su iya kaiwa Finikiya, wata mafakar tsibirin Karita, mai duban gabas maso arewa da kuma gabas maso kudu, su ci damuna a can.
13Da iska ta buso daga kudu sannu sannu, a tsammaninsu muradinsu ya biya ke nan, sai suka janye anka suka bi ta gefen tsibirin Karita gab da gaci. 14Ba da jimawa ba, kuwa dai ga wata gawurtacciyar iska da ake kira Yurokilidon ta bugo daga tsibirin. 15Da iskar ta bugo jirgin, har ya kasa fuskantarta, sai muka sallama mata, ta yi ta kora mu. 16Da muka bi ta jikin wani ɗan tsibiri mai suna Kauda muka samu muka yi iko da ƙaramin jirginmu da ƙyar. 17Bayan da suka jawo ƙaramin jirgi zuwa cikin babban jirgi, sai suka yi dabara suka ɗaɗɗaura igiyoyi ta gindin babban jirgin, suka rage shi. Don kuma gudun kada a fyaɗa su a yashin nan na Sirtis mai haɗiye kome, suka sauke filafilai, aka kora jirgin haka. 18Saboda hadiri yana sa mu tangaɗi ƙwarai da gaske, kashegari sai suka fara watsar da kayan da jirgin ya ɗauko, a ruwa. 19A rana ta uku kuma, su da kansu suka jefar da kayan aikin jirgin. 20Da dai muka yi kwana da kwanaki ba mu ga rana ko taurari ba, gawurtacciyar iskar hadiri kuma ta yi ta bugunmu, sai muka fid da zuciya daga tsira.
21Da yake an daɗe ba cin abinci, sai Bulus ya miƙe a tsaye a tsakiyarsu, ya ce, “Ya ku jama'a, da kun ji maganata, da ba ku taso daga tsibirin Karita kun fāɗa wannan masifa da hasara ba. 22To, a yanzu, ina yi muku gargaɗi ku yi ƙarfin hali, don ba wanda zai yi hasarar ransa a cikinku, sai dai a yi hasarar jirgin. 23Don a daren jiya mala'ikan Allah wanda ni nasa ne, nake kuma bauta masa, ya tsaya kusa da ni, 24ya ce, “‘Kada ka ji tsoro Bulus, lalle za ka tsaya a gaban Kaisar, ga shi kuma, Allah ya amsa ya yardar maka duk abokan tafiyarka su tsira.” 25Saboda haka, sai ku yi ƙarfin hali, ya ku jama'a, domin na gaskata Allah a kan cewa, yadda aka faɗa mini ɗin nan, haka za a yi. 26Amma fa lalle ne a fyaɗa mu a wani tsibirin.”
27A dare na goma sha huɗu, ana ta kora mu sakaka a bahar Adariya, wajen tsakar dare sai masu tuƙi suka zaci mun yi kusa da ƙasa. 28Sai suka gwada zurfin ruwan, suka sami gaba ashirin, da muka ci gaba kaɗan, sai suka sāke gwadawa, suka sami gaba goma sha biyar. 29Don gudun kada a fyaɗa mu a kan duwatsu, sai suka saki anka guda huɗu na bayan jirgin, suka ƙagauta gari ya waye. 30Masu tuƙi suna neman gudu daga jirgin ke nan, har sun zura ƙaramin jirgi a cikin ruwa, don a ga kamar za su ja su anka ɗin ne daga goshin jirgin su sake su, 31sai Bulus ya ce da jarumin yaki da kuma sojan. “In mutanen nan ba su tsaya a cikin jirgin nan ba, ba yadda za a yi ku tsira.” 32Sai sojan suka yayyanke igiyoyin ƙaramin jirgin, suka bar shi ya bi ruwa.
33Da gari ya yi kusan wayewa sai Bulus ya roƙe su su taɓa ɗan abinci, ya ce, “Yau fa kwana goma sha huɗu ke nan kuke zaman jira, ba wani abin da kuka ci. 34Saboda haka, ina roƙonku ku ci abinci, don lafiyarku, tun da yake ba wanda ko gashin kansa zai yi ciwo a cikinku.” 35Da ya faɗi haka, ya ɗauki curin gurasa, ya yi godiya ga Allah a gabansu duka, sa'an nan ya gutsuttsura ya fara ci. 36Sai duk suka farfado, su ma kansu suka ci abinci. 37Mu duka a cikin jirgin kuwa mutum metan da saba'in da shida ne. 38Da suka ci suka ƙoshi, sai suka riƙa rage wa jirgin nauyi, suka yi ta zub da alkama a cikin ruwa.
39Da gari ya waye ba su shaida ƙasar ba, amma dai sun lura da wani lungu da gaci mai yashi, sai kuma suka yi shawara cewa in mai yiwuwa ne su kai jirgin kan yashin. 40Sai suka daddatse su anka duka, suka bar su a ruwa, suna kuma ɓalle maɗaurin abin juyar da jirgin a lokacin, sa'an nan kuma suka ta da filafilan goshin jirgin daidai iska, suka doshi gaci. 41Amma da muka isa wata mahaɗar ruwa, sai suka tura jirgin ya dunguri yashi, har goshinsa ya cije ya kasa motsi, ƙarshensa kuma ya fara ragargejewa saboda haukan raƙuman ruwa. 42Sai sojan suka yi niyya su kashe 'yan sarka, don kada wani ya yi ninƙaya ya tsira. 43Amma jarumin da ya so ya ceci Bulus, ya hana i da nufinsu, ya kuma yi umarni duk waɗanda suka iya ruwa su fara fāɗawa zuwa gaci, 44sauran kuwa waɗansu suka hau katako, waɗansu kuma suka hau tarkacen jirgin. Da haka duk suka kai gaci lafiya.
1Bayan da muka tsira, sai muka ji, ashe, sunan tsibirin nan Malita ne. 2Mutanen garin kuwa sun yi mana alheri matuƙar alheri, don sun hura wuta sun karɓe mu, mu duka, saboda ana ruwa, ga kuma sanyi. 3Sa'ad da Bulus ya tattaro waɗansu ƙirare rungume guda ya sa a wutar, sai ga wani maciji ya bullo saboda zafi, ya ɗafe masa a hannu. 4Da mutanen garin suka ga mugum ƙwaron nan a makale a hannun Bulus, suka ce wa juna, “Lalle mutumin nan mai kisankai ne, kun ga ko da yake ya tsira daga bahar, duk da haka alhaki yana binsa sai ya mutu.” 5Bulus kuwa ya karkaɗe ƙwaron a cikin wutar, bai kuwa ji wani ciwo ba. 6Su kuwa suna zaton wurin zai kumbura, ko kuwa farat ɗaya ya fāɗi matacce. Amma da aka daɗe suka ga ba abin da ya same shi, suka sāke magana suka ce lalle shi wani Allah ne.
7A nan kusa kuwa akwai wani fili, mallakar shugaban tsibirin nan, mai suna Babiliyas. Shi ne ya karɓe mu, ya sauke mu a cikin martaba har kwana uku. 8Ashe, mahaifin Babiliyas yana a kwance, yana fama da zazzaɓi da ciwon atuni. Sai Bulus ya shiga wurinsa ya yi addu'a, ya ɗora masa hannu ya warkar da shi. 9Da aka yi haka sai duk sauran marasa lafiya a tsibirin suka riƙa zuwa ana warkar da su. 10Suka yi mana kyauta mai yawa, da za mu tashi a jirgin ruwa kuma, suka yi ta tara mana duk irin abubuwan da muke bukata.
11Bayan wata uku muka tashi a cikin wani jirgin Iskandariya, wanda ya ci damuna a nan tsibirin. An kuwa yi masa alama da surar Tagwaye Maza. 12Da muka zo Sirakusa muka kwana uku a nan. 13Daga nan kuma muka zaga sai ga mu a Rigiyum. Da muka kwana, iska ta taso daga kudu, kashegari kuma muka kai Butiyoli. 14A nan muka tarar da waɗansu 'yan'uwa, suka roƙe mu mu kwana bakwai tare da su. Da haka dai har muka isa Roma. 15Da 'yan'uwa na can suka ji labarinmu, sai da suka zo don su tarye mu har Kasuwar Abiyus, da kuma wurin nan da ake kira Maciya Uku. Da kuwa Bulus ya sadu da su, ya yi godiya ga Allah, jikinsa kuma ya yi ƙarfi. 16Da muka shiga Roma aka yardar wa Bulus ya je ya sauka abinsa tare da sojan da yake tsaronsa.
17Bayan kwana uku ya kira manyan Yahudawan birnin. Da suka taru sai ya ce musu, “Ya ku 'yan'uwa, ko da yake ban yi wa jama'armu wani laifi ba, ko laifi a game da al'adun kakanninmu, duk da haka an bashe ni ɗaurarre ga Romawa tun daga Urushalima. 18Su kuwa da suka tuhume ni, suna so su sāke ni, don ban yi wani laifi da ya isa kisa ba. 19Amma da Yahudawa suka ƙi yarda, sai ya zamar mini dole in nema a ɗaukaka ƙarata gaban Kaisar, ba don ina ƙarar jama'armu ba ne. 20Shi ya sa na nema in gana da ku, tun da yake dai saboda sa zuciyar nan da Isra'ila take yi ne nake ɗaure da sarƙan nan.” 21Sai suka ce masa, “Mu kam, ba mu sami wata wasiƙa daga Yahudiya a game da kai ba, ba kuwa wani ɗan'uwanmu da ya zo nan ya kawo labarinka, ko ya faɗi wata mummunar magana a game da kai. 22Amma muna so mu ji daga bakinka abin da yake ra'ayinka, don in dai ta ɗariƙar nan ne, mun sani ko'ina ana kushenta.”
23Da suka sa masa rana, sai suka zo masaukinsa, su da yawa. Sa'an nan ya yi ta yi musu bayani, yana ta shaidar musu Mulkin Allah, tun daga safe har magariba, yana ƙoƙarin rinjayarsu a kan Yesu, ta hanyar Attaurar Musa da littattafan annabawa. 24Waɗansu sun rinjayu da maganarsa, amma waɗansu sun ƙi gaskatawa. 25Da suka kasa yarda a junansu, kafin su watse sai Bulus ya yi musu magana ɗaya ya ce, “Ashe kuwa, Ruhu Mai Tsarki ya faɗa, da ya yi wa kakanninku magana ta bakin Annabi Ishaya cewa, 26“‘Je ka wurin jama'ar nan, ka ce, Za ku ji kam, amma ba za ku fahimta ba faufau, Za ku gani kuma, amma ba za ku gane faufau. 27Don zuciyar jama'ar nan ta yi kanta, Sun toshe kunnuwansu, Sun kuma runtse idanunsu, don kada su gani da idanunsu, Su kuma ji da kunnuwansu, Su kuma fahimta a zuciyarsu, Har su juyo gare ni in warkar da su.” 28To, sai ku sani, wannan ceto na Allah, an aiko da shi har ga al'ummai, su kam za su saurara.”
29(Da ya faɗi haka, sai Yahudawa suka tashi suna ta muhawwara da juna.)
30Sai Bulus ya zauna a nan a gidan da yake haya, har shekara biyu cikakku, yana maraba da duk wanda ya je wurinsa, 31yana ta wa'azin Mulkin Allah, da koyar da al'amarin Ubangiji Yesu Almasihu gabagaɗi, ba tare da wani hani ba.