DANIYEL
3. Adduar Azariya [Ga ƙari a Littafin Daniyel a sura ta 3 tsakanin aya ta 23 da 24]
1 Da aka watsa samarin cikin tanderu mai gagarumar wuta, sai suka yi ta rawa a tsakiyar wutar, har suka raira waƙar yabon Allah, suna girmama Ubangiji. 2 Sai Azariya ya tashi tsaye, ya yi wannan addua a tsakiyar wuta. Ga abin da va ce:
3 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji,
Allah na kakanninmu,
Ka ma cancanci yabo,
I, sunanka kuma ɗaukakakke ne har abada.
4 Gama kai mai adalci ne a dukan abubuwan da ka yi,
Dukan ayyukanka suna da gaskiya.
Hanyoyinka kuma ba su da aibu,
Ai, dukan shariunka na zahiri ne.
5 Shariar da ka yi mana, ai, duk ta gaskiya ce,
Haka ma wadda ka yi wa Urushalima,
Wato tsarkakakken birnin nan na kakanninmu.
Bisa ga gaskiya da adalci ne ka auko duk wannan abu a kanmu saboda zunubanmu.
6 Ai, ta zunubanmu da ƙin manufa ne muka bauɗe maka,
Mun yi saɓo a kowane abu.
Ba mu yi biyayya da dokokinka ba,
7 Ba mu bi su ba, ko mu kiyaye abin da suka ce,
Wanda ka umarce mu mu zauna lami lafiya.
8 Don haka duk abin da ka jibgo mana
Da wanda duk ka yi mana,
Ai, da adalci da gaskiya ne ka yi.
9 Ka ba da mu a hannun magabtan da ba su san abin da ya kamata ba,
Ranmu, ko kaɗan, bai kwanta da su ba.
Ka danƙa mu a hannun mugun sarki,
Duk duniyan nan, ba wanda ya kai shi ƙeta.
10 Yanzu ba mu iya ko buɗe bakinmu,
Kunya da ƙasƙanci sun auka wa bayinka, masu yi maka bauta.
11 Don darajar sunan nan naka,
Kada ka ba da mu kwatakwata,
Kada ma ka zare yarjejeniyarka.
12 Kada ma ka janye jinƙanka daga gunmu,
Saboda Ibrahim ƙaunataccenka,
Da kuma Ishaku bawanka,
Da mai tsarkin nan naka, Israila,
13 Waɗanda ka yi alkawari ta kansu, cewa
Jikokinsu za su yi yawan gaske kamar taurarin sama,
Har su yi yawan rairayin da ke bakin teku.
14 Gama mu yanzu, ya Ubangiji, mun fi sauran alumma salwanta,
An ma yi mana ƙasƙanci kwanan nan a dukan duniya
Saboda zunubanmu ne kuwa.
15 A wannan lokaci ma ba mu da sarki, ko annabi, ko shugaba,
Ba hadayar ƙonawa, ko wata irin hadaya, ko sadaka, ko turaren ƙonawa,
Ba gun da za a miƙa hadaya a gabanka, ko neman jinƙai.
16 Duk da haka, don muna da karyayiyyar zuciya da ruhun tuba,
Ai ka karɓe mu.
17 Kamar dai yadda ka karɓi hadayun ƙonawa na raguna da na bijimai,
Da kuma na yayan raguna masu kiɓa dubbai bisa dubbai,
Haka ma ka karɓi hadayarmu ta yau,
Domin muna binka sau da ƙafa.
Gama duk wanda ya dogara gare ka,
Ko kadan ba zai kunyata ba.
18 Yanzu mun bi ka da dukan zuciya,
Kanmu ƙasa, hannumnu baya, muna neman fuskarka.
19 Kada ka sa mu mu kunyata,
Amma ka rufa mana asiri ta haƙurinka,
Da kuma yawan jinƙanka.
20 Ka fanshe mu ta ayyukanka na alajabi,
Ka kuma sa a ɗaukaka sunanka, ya Ubangiji.
21 Ka sa duk waɗanda suka nufi su yi wa bayinka lahani, su kunyata,
Ka sa a ƙasƙanta su a hana su dukan iko da mulki,
Ka kuma buge musu gwiwoyi.
22 Ka sa su sani kai ne Ubangiji, Allah Makadaici,
Wanda dukan duniya ke ɗaukakawa.23 Lokacin da Azariya ke yin adduan nan, bayin sarkin da suka angaza su a wutar, ba su daina zuba wa wutar farar wuta, da baƙin mai, da yayi, da faskare ba. 24 Sai harshen wutar ya hau daga tanderu, har kamu arbain da tara. 25 Ta haɓaka, ta lashe Kaldiyawa waɗanda ke kewaye gagarumar wutar. 26 Amma wani malaikan Ubangiji ya gangara cikin tanderun tare da Azariya da abokansa, ya kori wuta daga tanderun. 27 Sai ya mai da tsakiyar tanderun kamar iska mai sanyi, ya zama har wutar ba ta taɓa su ba ko kaɗan, ba ta yi musu lahani ko wahala ba. 28 Saan nan su uku, da murya ɗaya, sai suka raira waƙa ga Allah, suka girmama shi, suka yabe shi a tsakiyar tanderun. Ga abin da suka ce:
Wakar Samari Uku
29 Yabo ya tabbata gare ka, Ya Ubangiji Allah na kakanninmu,
A yabe ka, a girmama ka har abada.
30 Yabo ya tabbata a gare ka, Sunanka mai tsarki yana da daraja,
A yabe ka, a girmama ka har abada.
31 Yabo ya tabbata gare ka a Haikalin ɗaukakarka mai tsarki,
A yabe ka, a girmama ka har abada.
32 Yabo ya tabbata gare ka, a bisa kursiyinka,
A yabe ka, a girmama ka har abada.
33 Yabo ya tabbata gare ka, Wanda ke zaune a bisa kerubobi,
A yabe ka, a girmama ka har abada.
Yabo ya tabbata gare ka, Mai duba zurfin duniya,
A yabe ka, a girmama ka har abada.
34 Yabo ya tabbata gare ka a sararin sama,
A yabe ka, a girmama ka har abada.
35 Ku yabi Ubangiji, ku ayyukan Ubangiji duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
36 Ku yabi Ubangiji, ku malaikun Ubangiji duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
37 Ku yabi Ubangiji, ku sammai da birbishin ƙasa,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
38 Ku yabi Ubangiji, ku ruwaye birbishin duniya,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
39 Ku yabi Ubangiji, ku dukan ikokin Allah,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
40 Ku yabi Ubangiji, ku rana da wata masu haske,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
41 Ku yabi Ubangiji, ku taurarin sama duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
42 Ku yabi Ubangiji, ku tsattsafi da raɓa duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
43 Ku yabi Ubangiji, ku iska da hadiri duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
44 Ku yabi Ubangiji, ku gumi da wuta duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
45 (Ku yabi Ubangiji, ku rani da damuna duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
46 Ku yabi Ubangiii, ku raɓa da ruwan sama duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.)
47 Ku yabi Ubangiji, ku jaura da sanyi duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
48 Ku yabi Ubangiji, ku ƙankara da dusan ƙanƙara duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
49 Ku yabi Ubangiji, ku dare da rana duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
50 Ku yabi Ubangiji, ku haske da duhu duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
51 Ku yabi Ubangiji, ku walkiya da girgije duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
52 Ku yabi Ubangiii, ku duniya duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
53 Ku yabi Ubangiji, ku duwatsu da tuddai duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
54 Ku yabi Ubangiii, ku mabunƙusa ƙasa duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
55 Ku yabi Ubangiji, ku maɓuɓɓugan ruwa duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
56 Ku yabi Ubangiii, ku tekuna da koguna duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
57 Ku yabi Ubangiji, ku kifaye manya da ƙanana,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
58 Ku yabi Ubangiji, ku tsuntsayen sama duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
59 Ku yabi Ubangiii, ku dabbobin duniya duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
60 Ku yabi Ubangiji, ku yan adam duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
61 Ku yabi Ubangiii, ku Israilawa duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
62 Ku yabi Ubangiji, firistocin Ubangiji duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
63 Ku yabi Ubangiji, ku bayin Ubangiji duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
64 Ku yabi Ubangiji, ku masu halin adalci duka,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
65 Ku yabi Ubangiji, ku tsarkaka masu sanyin hali
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
66 Ku yabi Ubangiji, Hananiya, da Azariya, da Mishayel,
Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.
Gama ya ƙwato mu daga lahira,
Ya fanshe mu daga mutuwa,
Ya kuɓutar da mu daga gagarumin tanderu duk da azabarta.
67 Ku yi wa Ubangiji godiya, gama shi mai alheri ne,
Jinƙansa ma yana ɗorewa har abada,
68 Ku yabi Allah da ke bisa alloli duka,
Ku yabe shi, ku yi masa godiya,
Gama jinƙansa yana ɗorewa har abada abadin.13. Labarin Suzana
1 A zamanin da, an yi wani mutum da ya zauna a Babila mai suna Yowakim. 2 Ya auri wata mace mai suna Suzana, yar Hilkiya, wata kyakkyawa ce mai tsoron Ubangiji. 3 Iyayenta adalai ne, sun kuma reni yarsu bisa ga Attaura ta Musa. 4 Yowakim mai wadata ne ƙwarai, yana da wani kyakkyawan lambu kusa da gidansa, Yahudawa sukan ziyarce shi a kai a kai, don duk ya fi su martaba.
5 A shekaran nan aka zaɓi mutum biyu su zama alƙalai. A kansu ne ma Ubangiji ya ce, Daga Babila ne shaicranci ya zo, daga dattawan da aka naɗa alkalai, waɗanda ya kamata su shugabanci jamaa. 6 Duk masu son kai ƙara suna zuwa gun mutanen nan. Su alkalan kuma suna zuwa gidan Yowakim a kai a kai. 7 Kowace rana, da maziyarta suka ba da baya da rana, sai Suzana ta tafi yawon miƙe ƙafa a lambun mijinta. 8 Dattawan nan biyu sun saba ganinta kowace rana, tana tafiyar lambun, tana yawace‑yawacenta. Ai, fa sai suka fara shaawar kyanta. 9 Sun tayar da lamirinsu, sun ƙi ko duba sama, ko tuna da dokokin adalci. 10 Su duka biyu suna ƙyashinta, amma ba su gaya wa juna suna sonta ba, 11 gama suna jin kunyar gaya wa juna yadda kowannensu ke so ya kwana da ita. 12 Har ma sun ƙagauta, kowace rana, sai zuba mata ido suke yi.
13 Wata rana sai suka ce wa junansu, Kai, mu tafi gida mana, ai, an gama abinci. Da suka fita waje, sai suka rabu da juna. 14 Amma kowannensu ya koma gidan su Suzana, duk sai suka sāke haɗuwa. Suka ce wa juna, Me ya sa haka? Sai suka magantu kan shaawarsu. Saan nan sai suka shawarta lokacin da za su iya samunta, ita kadai.
15 Wata rana, lokacin da suke zaman tsammani, sai ta shiga lambun kamar yadda ta saba yi da yan mata biyu kawai, tana shirin wanka cikin lambu, don ana jiɓi. 16 Ba kowa ke wurin sai dattawan nan biyu, waɗanda suka ɓoye, suna leƙenta. 17 Sai ta ce wa yan matanta, Ku miƙo mini sabulu da man shafawa, ku kuma rufe ƙofofin lambun don in yi wanka. 18 Suka yi kamar yadda ta ce, suka rufe ƙofofin, suka fita ta ƙofar gida domin su kawo abubuwan da aka umarce su, ba su ma ga dattawan nan ba, don sun ɓoye a ciki.
19 Da yan matan suka fita waje, sai dattawan nan biyu suka ruga gunta, suka ce, 20 Ke, ki duba, an rufe ƙofofin lambun dai, ba wanda zai ganmu. To, muna shaawarki, ki yardar mana, ki sam mana ma taɓa. 21 In kika ƙi, za mu dafa miki, mu ce wani saurayi ya yi lalata da ke, har mu ce don haka ne ma kika koro yan matanki waje.
22 Sai Suzana ta yi ajiyar zuciya ƙwarai, ta ce, Kun kewaye ni ta koina. In kuwa na yi wannan abu, mutuwa zan yi, in ban yi ba kuma, ba zan iya kuɓuce muku ba. 23 Ba zan yi abin ba, gara ku yi mini ɗaukakakkiyar da kuka ce, da in yi zunubi a gaban Ubangiji. 24 Saan nan Suzana ta fasa ƙara da kakkausar murya, sai dattawan nan biyu suka yi mata ihu. 25 Har ma gudansu ya ruga, ya buɗe ƙofar lambun. 26 A lokacin da bayi maza na gida suka ji kururuwa cikin lambun, sai suka yiwo dandazo ƙofar gida, su ga abin da ya same ta. 27 Da dattawan nan suka gaya wa bayin ƙagen, sai bayin suka ji kunyar gaske, don abin kunya irin wannan bai taɓa faɗa wa Suzana haka ba.
28 Kashegari da jamaa suka taru a gidan mijinta, wato Yowakim, sai dattawan nan biyu suka zo, don tsananin ƙeta suna so su sa a kashe Suzana. 29 Suka ce wa jamaa, Ku kira mana Suzana, yar Hilkiya, matar Yowakim. 30 Aka aika wa Suzana. 31 Sai ta zo, har ma da iyayenta da yayanta da dai dukan danginta. 32 Suzana ya ce mai kyan diri, ga kyau, sai ka ce aIjana. 33 Tana da lulluɓi, sai shaiɗanun nan suka ce a kware lulluɓin domin su ƙara kallon kyanta a tsanaki. 34 Amma da iyayenta, da dai duk sauran dangi, kowa ya gan ta, sai ta fashe da kuka.
34 Daganan dattawan nan biyu suka tsaya a tsakiyar jamaa, suka tsira wa Suzana hannu. 35 Da ta fara kuka, sai ta ɗaga kai sama, gama ta amince da Ubangiji da dukan zuciyarta. 36 Sai manyan gwazar suka ce, Muna yawo cikin lambu mu kaɗai, sai matan nan ta shigo lambun da yan mata guda biyu, ta rufe ƙofofin lambun, saan nan ta kori yan mata biyu ɗin. 37 Nan da nan sai wani saurayi, da ke ɓoye a lambun, ya je gunta, suka yi lalata. 38 Mu kuwa muna laɓe a kusurwar dami, da muka ga wanhan mugun abu, sai muka ruga don mu hana su. 39 Muka tarar sun ƙulle, amma ba dama mu taɓa namijin, don ya fi ƙarfinmu, sai ya buɗe ƙofa ɓagas, ya shara da gudu. 40 Sai muka riƙe ta, muka ce ta gaya mana sunan saurayin. 40 Amma ta ƙi. Abin da muka shaida ke nan. Sai taron ya gaskata, domin su dattawan jamaa ne, alƙalai kuma. Suka hukunta mata mutuwa.
42 Sai Suzana ta yi kururuwa da ƙarfi, ta ce, Ya Allah Madawwami, wanda ka san abin da ke ɓoye, ka san dukan abubuwa kafin ma su faru, 43 ka sani dai mutanen nan ƙage ne kawai suka yi mini. Ga shi, an hukunta mini mutuwa! Duk da haka ban yi ko ɗaya daga cikin abubuwan da suka ƙaga mini ba!
44 Sai Ubangiji ya ji roƙonta. 45 Ana tafiya da ita ke nan inda za a kashe ta, sai Allah ya iza tsattsarkan ruhu na wani saurayi mai suna Daniyel. 46 Ya yi kira da murya mai ƙarfi, ya ce, Ba ruwana da jinin macen nan mai adalci.
47 Sai dukan jamaa suka waige shi, suka ce, Me kake cewa haka?
48 Da ya tsaya a tsakiyarsu, sai ya ce, Ashe, ku mutanen nan na Israila wawaye ne haka? Kun hukunta wa yar Israila mutuwa kawai, ba tare da binciken gaskiyar abin ba? 49 Ku dai koma fadar! Ai, mutanen nan ƙagen ƙarya ne suka yi mata kawai.
50 Sai dukan mutane suka dawo da gaggawa. Dattawan kuma suka ce masa, Zo, ka zauna nan a gabanmu, ka gaya mana gaskiya. Ai, kai ne ka yanke wa ƙasa cibiya!
51 Amma Daniyel ya ce wa taron, Ku raba alƙalan nan nesa da juna, zan jarraba su in gani.
52 Da aka raba su da juna, sai ya kirawo ɗayansu, ya ce masa, Kai, tsohon dattijon burgu, zunubanka sun tonu, waɗanda ka taɓa yi duka. 53 Kana yin shariar sonkai, kana hukunta adalai, ka ƙyale shaiɗanu, ko da ya ke Ubangiji ya ce, Kada ka hukunta adali marar aibu. 54 To yanzu, in dai ka tabbata ka gan ta, gaya mini gaskiya, ƙarƙashin wane itace ne ka ga sun ƙulle?
Ya amsa, ya ce, A ƙarƙashin itacen kargo.
55 Sai Daniyel ya ce, To madalla! Bakinka ya yanka wuyanka, gama malaikan Allah ya karɓo hukuncinka daga gun Allah, yanzu zai datsa ka biyu.
56 Saan nan ya kawar da wannan waje ɗaya, ya umarci a kawo gudan. Ya ce wa gudan, Kai jikan Kanana ne, ba na Yahuza ba, kyau ya ruɗa ka, shaawa kuma ta cika zuciyarka. 57 Ai, haka ne ma kuke ta yi da yan matan mulkin Israila, dole ne kuwa suke yarda da ku, don suna jin tsoronku. Amma yarinyan nan ta mulkin Yahudiya ba ta yarda da saɓonku ba ko kaƙan. 58 Yanzu, sai ka gaya mini, ƙarƙashin wane itace ne ka ga sun ƙulle?
Ya amsa shi ma, ya ce, A ƙarƙashin wani itacen maje ne.
59 Sai Daniyel ya ce masa, Naam! Kai ma ka sheƙa karyar, bakinka ya yanka wuyanka, gama malaikan Allah yana jiranka da takobi, zai raba ka biyu, ya hallaka dukanku biyu.
60 Dukan taron ya yi wata irin gunza gaba ɗaya, ya yabi Allah wanda ke fansar waɗanda suke sa rai a gare shi. 61 Suka wanke hannu, suka auka wa dattawan nan biyu, gama Daniyel ya ƙure ƙaryar ƙagensu. Sai aka yi musu horon da suka yi niyyar yi wa Suzana 62 bisa ga shariar Musa, aka kashe su. Ta haka aka fanshi jinin adala ran nan.
63 Sai Hilkiya da matarsa suka yabi Allah a kan yarsu Suzana, haka Yowakim mijinta, da dukan danginta suka yi, da ya ke ba a same ta da abin kunya ba. 64 Tun daga ran nan ne Daniyel ya yi babban suna a cikin jamaa.
14. Labarin Bel da Babban Maciji
1 A lokacin da sarki Asatiyagas ya mutu, sai Sairus mutumin Farisa, ya hau gadon mulkin. 2 Daniyel kuwa abokin sarki ne. Sarkin kuwa ba shi da wani ingantaccen aboki kamar Daniyel. 3 A zamanin Babilawa suna da wani gunkin da suke kira Bel, kowace rana suna ba Bel garwar gari goma sha biyu, da tumaki arbain, da dasar giya hamsin. 4 Sarkin ya yi naam da Bel, har yana yi masa sujada a kowace rana. Amma Daniyel yana bauta wa Allahnsa mai gaskiya. 5 Sai sarkin ya ce wa Daniyel, Don me ba ka bauta wa Bel ba?
Daniyel ya ce, Domin ban yi naam da gumakan da yan adam suka yi ba, sai dai Allah rayayye kaɗai, wanda ya halicci sama da ƙasa, yana kuma da iko bisa kowane mutum.
6 Sarkin ya ce masa, Ba ka ɗauki Bel shi ne allah rayayye ba? Ba ka ga abincin da yake dankara kowace rana ba, ga giya kuma?
7 Sai Daniyel ya yi dariya, ya kuma ce, Kada ka ruɗi kanka, ya sarki, gama wannan yumɓu ne kawai aka dalaye da jan ƙarfe. Ai, ba ya ma iya ci ko shan wani abu.
8 Sai sarkin ya husata, ya kira firistocinsa, ya ce musu, In ba ku gaya mini wanda ke cin kayan nan ba, to, za ku baƙunci lahira. 9 Amma in kun nuna mini yadda Bel ke cinye su, zan kashe Daniyel, gama ya saɓi Bel.
Sai Daniyel ya ce wa sarkin, A yi abin da ka umarta mana.
10 Akwai firistoci har sabain na Bel, banda matansu da yayansu.
Sai Sarki ya tafi da Daniyel har haikalin Bel. 11 Firistoci na Bel suka ce, Duba, yanzu za mu fita waje. Kai da kanka, ya sarki, kai ne za ka haɗa abincin, ka kuma ajiye giyar. Saan nan ka rufe ƙofar, ka hatimce ta da hatiminka. 12 Gobe in ka dawo da safe, har in ba ka tarar Bel ya naɗe su ba, mun yarda mu mutu, ko kuma Daniyel ya mutu, wanda yake māka mana ƙarya. 13 Ba ruwansu, gama a ƙarkashin teburin sun yi rami ta inda suke shiga kullum, suna cinye dukan abincin nan. 14 Da suka fita waje, sai sarkin ya shirya wa Bel abincin. Saan nan Daniyel ya umarci bayi su kawo toka su barbaɗa ta cikin dukan haikali a idon sarki, shi kaɗai. Saan nan suka fita waje, suka rufe ƙofar, suka sa hatimin sarki, suka kawar da jiki. 15 Da dare ya tsala, sai firistoci suka fito, su da matansu, da yayansu kamar dai yadda suka saba yi, suka cinye dukan abincin suka shanye giyar.
16 Da sassafe sai sarki ya taso, ya zo, da shi da Daniyel. 17 Sarki ya ce, An huje hatimin, Daniyel?
Daniyel ya ce, Aa, ranka ya daɗe.
18 Da dai aka buɗe ƙofar, Sarki ya duba teburin, sai ya yi kira da ƙarfi, ya ce, Ai, mai girma kake, ya Bel, ba ka ruɗin kowa, aa, ko kaɗan.
19 Sai Daniyel ya yi dariya, ya hana sarki shiga, ya ce masa, Dubi daɓen ɗakin, ka kula, sawun suwanene nan?
20 Sarki ya ce, Ni dai na ga sawun maza, da na mata, da yayansu. 21 Sai sarkin ya husata, ya matsa wa firistoci, da matansu, da yayansu, sai da suka nuna masa ɓoyayyiyar ƙofar da suka saba bi, suna cinye dukan abin da ke kan teburin. 22 Sai sarki ya sa aka kashe su, kana kuma ya ba Daniyel Bel ɗin, Daniyel kuwa ya lalata Bel duk da haikalinsa.
23 Akwai ma wani gawurtaccen maciji da Babilawa suka yi naam da shi. 21 Sarki ya ce wa Daniyel, Ba ka iya shakkar wannan allah ne rayayye, don haka ka bauta masa mana.
25 Daniyel ya ce, Zan bauta wa Ubangiji Allahna, gama shi ne Allah rayayye. 26 In kai dai, sarki, za ka ba ni dama, zan yanka macijin nan, ba tare da takobi ko kuma kulki ba.
Sarkin ya ce, Na ba ka iznin.
27 Sai Daniyel ya ɗauki baƙin mai, da kitse, da gashi, ya dafa su tare, ya yi waina, wadda ya ciyar da macijin da ita. Macijin ya ci wainar, har cikinsa ya fashe. Daniyel ya ce, Kai jamaa, dubi abin da kuke ta bauta wa!
28 Da Babilawa suka ji haka fa, sai suka ji haushi kwarai, suka kuma yi shirin kashe sarkin, suka ce, Ai, sarkin nan namu ya zama Bayahude, ya yi kacakaca da Bel, ya kuma kashe macijin, ya yanyanka sarkin tsafinsa. 29 Da suka isa gun sarkin, sai suka ce masa, Ka hannanta mana Damyel, ko kuwa mu kashe ka, kai da dukan iyalin gidanka. 30 Sarki fa, da ya ga sun matsa masa, sai ya hannanta musu Daniyel tilas. 31 Sai suka jefa Daniyel a ramin zakoki, har ya kwana shida a can ciki. 32 Akwai zakoki bakwai a ramin nan nasu. Abincin zakokin kuwa, shi ne kowace rana a ba su mushen mutum biyu da tumaki biyu, amma yanzu an hana musu, domin su cinye Daniyel.
33 A lokacin, annabi Habakuk yana Yahudiya. Sai ya ɗunɗuma abinci, ya gutsuttsura gurasa a kwanon, ya ɗauka, zai kai wa yan girbi a gona. 34 Amma wani malaikan Ubangiji ya ce wa Habakuk, Wannan gara da ka shirya, ai, sai ka kai ta Babila, ka ba Daniyel, wanda yake zaune a ramin zakoki.
35 Habakuk ya ce, Malam, ai, ni ban taɓa zuwa Babila ba, ban kuma san ramin ba. 36 Saan nan malaikan ya suri Habakuk ta gashin kansa, ya ɗauke shi sama, ya saka a garin Babila, gab da ramin, da hucin iska mai karfi.
37 Sai Habakuk ya yi kira, ya ce, Daniyel, Daniyel! Ci abincin nan da Allah ya aiko maka!
38 Daniyel ya ce, Kai ne ka tuna da ni, ya Allah, ai, ba ka mancewa da waɗranda ke kaunarka. Sai Daniyel ya tashi, ya ci abinci. Nan da nan kuma malaikan Ubangijin ya mai da Habakuk gidansu.
40 A rana ta bakwai sai sarki ya zo domin ya yi wa Daniyel makoki. Da ya iso ramin, ya leƙa, sai ya yi arangama da Daniyel a zaune. 41 Sai sarkin ya yi kwakwazo, ya ce, Ai, kai mai girma ne, ya Ubangiji na Daniyel, ba ma wani kamarka. 42 Ya zaro Daniyel waje, ya zuba mutanen da suka yi shirin kashe Daniyel a ciki. Nan da nan kuwa zakokin suka dira musu a idon sarki.
* * * * *
* * *
*